< Ishaya 3 >

1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
Car voici, le Seigneur, l'Eternel des armées, s'en va ôter de Jérusalem et de Juda le soutien et l'appui, tout soutien de pain, et tout soutien d'eau.
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
L'homme fort, et l'homme de guerre, le juge et le Prophète, l'homme éclairé sur l'avenir, et l'ancien.
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
Le cinquantenier, et l'homme d'autorité, le conseiller, et l'expert entre les artisans, et le bien-disant;
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
Et je leur donnerai de jeunes gens pour gouverneurs, et des enfants domineront sur eux.
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
Et le peuple sera rançonné l'un par l'autre, et chacun par son prochain. L'enfant se portera arrogamment contre le vieillard, et l'homme abject contre l'honorable.
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
Même un homme prendra son frère de la maison de son père, [et lui dira]; tu as un manteau, sois notre conducteur, et que cette dissipation-ci [soit] sous ta conduite.
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
[Et celui-là] lèvera [la main] en ce jour-là, en disant; je ne saurais y remédier, et en ma maison il n'y a ni pain ni manteau; ne me faites point donc conducteur du peuple.
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
Certes Jérusalem est renversée, et Juda est tombé; parce que leur langue et leurs actions sont contre l'Eternel, pour irriter les yeux de sa gloire.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
Ce qu'ils montrent sur leur visage rend témoignage contr'eux, ils ont publié leur péché comme Sodome, et ne l'ont point célé; malheur à leur âme, car ils ont attiré le mal sur eux!
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
Dites au juste, que bien lui sera: car [les justes] mangeront le fruit de leurs œuvres.
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
Malheur au méchant [qui ne cherche qu'à faire] mal; car la rétribution de ses mains lui sera faite.
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
Quant à mon peuple, les enfants sont ses prévôts, et les femmes dominent sur lui. Mon peuple, ceux qui te guident, [te] font égarer, et t'ont fait perdre la route de tes chemins.
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
L'Eternel se présente pour plaider, il se tient debout pour juger les peuples.
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
L'Eternel entrera en jugement avec les Anciens de son peuple, et avec ses Principaux; car vous avez consumé la vigne, et ce que vous avez ravi à l'affligé est dans vos maisons.
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
Que vous revient-il de fouler mon peuple, et d'écraser le visage des affligés? dit le Seigneur, l'Eternel des armées.
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
L'Eternel a dit aussi; parce que les filles de Sion se sont élevées, et ont marché la gorge découverte, et faisant signe des yeux, et qu'elles ont marché avec une fière démarche faisant du bruit avec leurs pieds,
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
L'Eternel rendra chauve le sommet de la tête des filles de Sion, et l'Eternel découvrira leur nudité.
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
En ce temps-là le Seigneur ôtera l'ornement des sonnettes, et les agrafes, et les boucles;
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
Les petites boîtes, et les chaînettes, et les papillotes;
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
Les atours, et les jarretières, et les rubans, et les bagues à senteur, et les oreillettes;
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
Les anneaux, et les bagues qui leur pendent sur le nez;
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
Les mantelets, et les capes, et les voiles, et les poinçons,
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
Et les miroirs, et les crêpes, et les tiares, et les couvre-chefs.
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
Et il arrivera qu'au lieu de senteurs aromatiques, il y aura de la puanteur; et au lieu d'être ceintes, elles seront découvertes, et au lieu de cheveux frisés, elles auront la tête chauve; et au lieu de ceintures de cordon, [elles seront ceintes] de cordes de sac; et au lieu d'un beau teint, elles auront le teint tout hâlé.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
Tes gens tomberont par l'épée, et ta force par la guerre.
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
Et ses portes se plaindront, et mèneront deuil; et elle sera vidée, et gisante par terre.

< Ishaya 3 >