< Ishaya 7 >

1 Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
Or il avint aux jours d'Achaz fils de Jotham, fils d'Hozias Roi de Juda, que Retsin Roi de Syrie, et Pékach fils de Rémalja Roi d'Israël, montèrent contre Jérusalem pour lui faire la guerre; mais ils ne la purent forcer.
2 Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
Et on rapporta à la maison de David, en disant; La Syrie s'est reposée sur Ephraïm. Et le cœur d'Achaz, et le cœur de son peuple fut ébranlé, comme les arbres des forêts sont ébranlés par le vent.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
Alors l'Eternel dit à Esaïe; Sors maintenant au-devant d'Achaz, toi, et Séar-Jasub ton fils, vers le bout du conduit du haut étang, vers le grand chemin du champ du foulon;
4 Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
Et lui dis; prends garde à toi, et demeure tranquille; ne crains point, et que ton cœur ne devienne point lâche à cause des deux queues de ces tisons fumants, à cause, [dis-je], de l'ardeur de la colère de Retsin et de la Syrie, et du fils de Rémalja.
5 Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
De ce que la Syrie a délibéré avec Ephraïm et le fils de Rémalja de te faire du mal, en disant;
6 “Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
Montons en Judée, et la réveillons, et nous y faisons ouverture, [partageons-la] entre nous, et établissons pour Roi le fils de Tabéal, au milieu d'elle.
7 Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
Ainsi a dit le Seigneur, l'Eternel; [cela] n'aura point d'effet, et ne se fera point.
8 gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
Car la Capitale de la Syrie c'est Damas, et le Chef de Damas c'est Retsin; et dans soixante-cinq ans Ephraïm sera froissé pour n'être plus un peuple.
9 Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
Et la Capitale d'Ephraïm c'est Samarie; et le Chef de Samarie c'est le fils de Rémalja, et si vous ne croyez [ceci], certainement vous ne serez point affermis.
10 Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
Et l'Eternel continua de parler avec Achaz, en disant;
11 “Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol h7585)
Demande un signe pour toi, de l'Eternel ton Dieu, demande[-le], soit au plus bas lieu, soit dans le plus haut. (Sheol h7585)
12 Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
Et Achaz dit; je n'en demanderai point, et je ne tenterai point l'Eternel.
13 Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
Alors [Esaïe] dit; ecoutez maintenant, ô Maison de David! Vous est-ce peu de chose de travailler les hommes, que vous travailliez aussi mon Dieu?
14 Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
C'est pourquoi le Seigneur lui-même vous donnera un signe; voici, une Vierge sera enceinte, et elle enfantera un fils, et appellera son Nom EMMANUEL;
15 In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
Il mangera du beurre et du miel, jusques à ce qu'il sache rejeter le mal, et choisir le bien.
16 Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
Mais avant que l'enfant sache rejeter le mal, et choisir le bien, la terre que tu as en détestation, sera abandonnée par ses deux Rois.
17 Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
L'Eternel fera venir sur toi, et sur ton peuple, et sur la maison de ton père, par le Roi d'Assur, des jours tels qu'il n'y en a point eu de semblables depuis le jour qu'Ephraïm se sépara de Juda.
18 A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
Et il arrivera qu'en ce jour-là, l'Eternel sifflera aux mouches qui sont au bout des ruisseaux d'Egypte, et aux abeilles qui [sont] au pays d'Assur.
19 Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
Et elles viendront, et se poseront toutes dans les vallées désertes, et dans les trous des rochers, et par tous les buissons, et par tous les halliers.
20 A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
Et ce jour-là, le Seigneur rasera avec le rasoir pris à louage au delà du fleuve, [savoir] avec le Roi d'Assur, la tête et les poils des pieds, et il achèvera aussi la barbe.
21 A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
Et il arrivera en ce temps-là qu'un homme nourrira une vache et deux brebis.
22 Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
Mais il arrivera que pour l'abondance du lait qu'elles rendront, il mangera du beurre; car tout homme qui sera demeuré de reste dans le pays, mangera du beurre et du miel.
23 A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
Et il arrivera en ce jour-là que tout lieu où il y aura eu mille vignes, de mille [pièces] d'argent, sera réduit en ronces et en épines.
24 Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
On y entrera avec des flèches et avec l'arc, car tout le pays [ne] sera [que] ronces et épines.
25 Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.
Et dans toutes les montagnes qu'on essartait avec la serpe, là on ne craindra plus de voir des ronces et des épines, mais ce sera pour y jeter les bœufs, et pour être foulé des brebis.

< Ishaya 7 >