< Ishaya 21 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
Profeti imod Havets Ørk. Ligesom Hvirvelvinde fare frem i Syden, saa kommer det fra Ørken, fra det forfærdelige Land.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
Mig er kundgjort et haardt Syn: Røveren røver, og Ødelæggeren ødelægger; drag op, Elam! træng paa Madaj! jeg har gjort, at hvert Suk hører op.
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
Derfor ere mine Lænder fulde af Smerter, Veer have betaget mig ligesom Veer den fødende; jeg vrider mig, saa jeg ikke kan høre, jeg er forfærdet, saa at jeg ikke kan se.
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
Mit Hjerte er forvildet, Gru har forfærdet mig, Tusmørket, som var min Lyst, er blevet mig til Rædsel.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
Man dækker Bord, Vagten vaager, man æder, man drikker; — „gører eder rede, I Fyrster! salver Skjoldet!‟
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
Thi saa sagde Herren til mig: Gak, sæt en Vægter ud, lad ham kundgøre, hvad han ser.
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
Og ser han Vogne, Ryttere parvis, Vogne, dragne af Asener, Vogne, dragne af Kameler, da skal han give Agt, nøje Agt.
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
Og han raabte som en Løve: Herre! jeg staar stadig paa Vagt om Dagen, jeg staar paa min Vare hver Nat.
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
Og se! da kom der Vogne med Folk, Ryttere parvis; og han svarede og sagde: Babel er falden, den er falden, og man har kastet alle dens Gudebilleder knuste til Jorden!
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
Du, min tærskede, og du, som har været lagt paa min Lo! det, jeg hørte af den Herre Zebaoth, Israels Gud, kundgjorde jeg eder.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
Profeti imod Duma. Der raaber en til mig fra Seir: Vægter, hvordan skrider Natten? Vægter, hvordan skrider Natten?
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
Vægteren siger: Der kommer Morgen, men ogsaa Nat; ville I spørge, saa spørger! kommer igen en anden Gang.
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
Profeti imod Arabien. I skulle blive Natten over i Skoven i Arabien, I rejsende Hobe af Dedaniter!
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
De komme den tørstige i Møde med Vand; Indbyggerne i Themas Land møde den flygtende med Brød.
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
Thi de flyede for Sværd, for det dragne Sværd, for den spændte Bue og for den svare Krig.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
Thi saa sagde Herren til mig: Endnu inden et Aar, som en Daglønners Aar, da skal al Kedars Herlighed faa Ende.
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
Og Tallet af Buerne, som blive tilbage for de vældige af Kedars Børn, skal formindskes; thi Herren, Israels Gud, har talt det.

< Ishaya 21 >