< Ishaya 2 >
1 Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
The word that Isaiah the son of Amoz foresaw concerning Judah and Jerusalem.
2 A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
And it shall come to pass in the last days, that the mountain of the Lord's house shall be firmly established on the top of the mountains, and shall be exalted above the hills; and unto it shall flow all the nations.
3 Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
And many people shall go and say, Come ye, and let us go up to the mountain of the Lord, to the house of the God of Jacob; that he may teach us of his ways, and we may walk in his paths; for out of Zion shall go forth the law, and the word of the Lord out of Jerusalem.
4 Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
And he will judge among the nations, and decide for many people; and they shall beat their swords into ploughshares, and their spears into pruning-knives: nation shall not lift up sword against nation, and they shall not learn any more war.
5 Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
O house of Jacob, come ye, and let us walk in the light of the Lord.
6 Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
For thou hast abandoned thy people, the house of Jacob, because they are full of [witchcraft] more than the east, and are soothsayers like the Philistines, and with the children of strangers they unite themselves.
7 Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
And full became their land of silver and gold, and there is no end to their treasures; and full became their land of horses, and there is no end to their chariots;
8 Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
And full became their land of idols; to the work of their own hands they bow themselves, to what their own fingers have made.
9 Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
And so is bent down the son of earth, and humbled the man; and thou wilt not forgive them.
10 Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
Enter into the rock, and hide thee in the dust, because of the dread of the Lord, and because of the glory of his majesty.
11 Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
The looks of human pride shall be humbled, and the haughtiness of men shall be bent down: and exalted shall be the Lord alone on that day.
12 Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
For there is a day [of judgment] unto the Lord of hosts over every proud and lofty one; and over every exalted one, that he be brought low;
13 domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
And over all the cedars of the Lebanon, the high and exalted, and over all the oaks of Bashan;
14 domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
And over all the high mountains, and over all the exalted hills;
15 domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
And over every high tower, and over every fortified wall;
16 domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
And over all the ships of Tharshish; and over all desirable palaces.
17 Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
And the pride of man shall be bent down, and the haughtiness of men shall be humbled: and exalted shall be the Lord alone on that day.
18 za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
And the idols will he utterly abolish.
19 Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
And men shall enter into the caverns of rocks, and into the rifts of the earth, because of the dread of the Lord, and because of the glory of his majesty, when he ariseth to terrify the earth.
20 A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
On that day shall a man cast away his idols of silver, and his idols of gold, which have been made for him to worship, to the moles and to the bats;
21 Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
To enter into the clefts of the rocks, and into the hollows of the cliffs, because of the dread of the Lord, and because of the glory of his majesty, when he ariseth to terrify the earth.
22 Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?
Withdraw yourselves [then] from man, whose breath is in his nostrils; because, for what is he to be esteemed?