< Ibraniyawa 5 >
1 Akan zaɓi kowane babban firist daga cikin mutane ne, akan kuma naɗa shi domin yă wakilce su a kan al’amuran Allah, domin yă miƙa kyautai da hadayu saboda zunubai.
For every high priest, who is from among men, is established over the things of God, in behalf of men, that he may present the offering and the sacrifices for sin:
2 Da yake babban firist ɗin mai kāsawa ne, yana iya bin da jahilai da kuma waɗanda suka kauce hanya, a hankali.
and he can humble himself, and sympathize with the ignorant and the erring, because he also is clothed with infirmity.
3 Shi ya sa dole yă miƙa hadayu domin zunubansa, da kuma domin zunuban mutane.
And, therefore, he is obliged as for the people, so also for himself, to present an offering for his sins.
4 Ba wanda yakan kai kansa a wannan matsayi mai girma; sai ko Allah ya kira shi, kamar yadda aka yi wa Haruna.
And no one taketh this honor on himself, but he who is called of God, as Aaron was.
5 Haka ma Kiristi bai kai kansa neman ɗaukaka na zama babban firist ba. Allah ne dai ya ce masa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka.”
So also the Messiah did not exalt himself to become a High Priest; but He appointed him who said to him, Thou art my Son; this day have I begotten thee.
6 Ya kuma ya ce a wani wuri, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn )
As he said also in another place: Thou art a priest for ever, after the likeness of Melchisedec. (aiōn )
7 A lokacin da Yesu ya yi rayuwa a duniya, ya yi addu’o’i da roƙe-roƙe tare da kuka mai zafi da kuma hawaye ga wannan wanda yake da ikon cetonsa daga mutuwa, aka kuwa ji shi saboda tsananin bangirman da ya yi.
Likewise, when he was clothed in flesh, he presented supplication and entreaty with intense invocation, and with tears, to him who was able to resuscitate him from death; and he was heard.
8 Ko da yake shi ɗa ne, ya yi biyayya ta wurin shan wahala
And though he was a son, yet, from the fear and the sufferings he endured, he learned obedience.
9 kuma da aka mai da shi cikakke, sai ya zama hanyar samun madawwamin ceto ga dukan waɗanda suke masa biyayya. (aiōnios )
And thus he was perfected and became the cause of eternal life to all them who obey him. (aiōnios )
10 Allah kuwa ya naɗa shi yă zama babban firist, bisa ga tsarin Melkizedek.
And he was named of God, the High Priest after the likeness of Melchisedec.
11 Muna da abubuwa masu yawa da za mu faɗa game da wannan batu, sai dai yana da wuya a bayyana, da yake ba ku da saurin ganewa.
Now, concerning this person, Melchisedec, we have much discourse, which we might utter; but it is difficult to explain it, because ye are infirm in your hearing.
12 Gaskiya, a yanzu ya kamata a ce kun zama malamai, sai ga shi kuna bukatar wani yă sāke koya muku abubuwa masu sauƙi game da abin da Allah ya faɗa. Kuna bukatar madara, ba abinci mai kauri ba!
For ye ought to be teachers, seeing ye have been long in the doctrine. But now ye need to learn again the first lines of the commencement of the oracles of God: and ye have need of milk, and not of strong food.
13 Duk wanda yake rayuwa a kan madara, shi kamar jariri ne har yanzu, kuma bai san ainihi mene ne ya dace ba.
For every one whose food is milk, is unversed in the language of righteousness, because he is a child.
14 Amma abinci mai kauri na balagaggu ne, waɗanda suka hori kansu don su bambanta tsakanin nagarta da mugunta.
But strong food belongeth to the mature who, being investigators, have trained their faculties to discriminate good and evil.