< Ibraniyawa 11 >

1 Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba.
Now faith is the confident expectation of things hoped for, and a conviction of things not seen:
2 Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.
for by it the ancients obtained an honorable testimony.
3 Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn g165)
By faith we understand that the worlds were framed by the word of God, for the things which are seen were not made of things which appear. (aiōn g165)
4 Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.
By faith Abel offered unto God a more excellent sacrifice than Cain, by which he obtained the testimony that he was righteous, God bearing witness to his gifts: and by it, though dead, he yet speaketh.
5 Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah.
By faith Enoch was translated, that he should not see death; and was not found, because God had translated him; for before his translation he had this testimony that he pleased God:
6 In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.
whereas without faith it is impossible to please Him; for he that cometh to God must believe, that He is, and is the rewarder of them that diligently seek Him.
7 Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.
By faith Noah being warned by God of things which were not yet seen, moved with pious fear, prepared an ark for the safety of his family; whereby he condemned the world, and became heir of the righteousness which is by faith.
8 Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba.
By faith Abraham when called to go out to a place which he was afterwards to receive for an inheritance obeyed: and went out, though he knew not whither he was going.
9 Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi.
By faith he sojourned in the land promised him, as in a foreign country, dwelling in tents, as did Isaac and Jacob the heirs with him of the same promise.
10 Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne.
For he looked for a city which hath foundations, whose maker and founder is God.
11 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne.
By faith also Sarah received strength to conceive seed, and brought forth a son when she was past age, because she accounted Him faithful who had promised.
12 Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.
So that there descended even from one, and him in a manner dead, a posterity like the stars of heaven for multitude, and as the sand on the sea shore, innumerable.
13 Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya.
These all died in faith, not having received the promises, but seen them from afar, and been persuaded of them, and embraced them, and confessed that they were strangers and sojourners on the earth.
14 Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
Now they that say such things shew plainly that they are seeking their own country:
15 Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
and if they had been mindful of that from which they came, they might have had opportunity to have returned.
16 A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
But they desire a better, that is, an heavenly one; wherefore God is not ashamed to be called their God; for He hath prepared for them a city.
17 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa,
By faith Abraham, when he was tried, offered up Isaac: and he who had received the promises, offered up his only son;
18 ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
of whom it was told him, that in Isaac shall thy seed be called:
19 Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.
concluding that God was able to raise him even from the dead; from whence indeed he had in a manner received him.
20 Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.
By faith Isaac blessed Jacob and Esau concerning things future.
21 Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.
By faith Jacob, when he was dying, blessed each of the sons of Joseph; and worshipped leaning on the top of his staff.
22 Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.
By faith Joseph when he died, mentioned the departure of the children of Israel and gave a charge concerning his bones.
23 Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.
By faith Moses, when he was born, was hid three months by his parents, because they saw he was a fine child, and they were not afraid of the king's edict.
24 Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna.
By faith Moses, when he was grown up, refused to be called the son of Pharaoh's daughter;
25 Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci.
chusing rather to suffer affliction with the people of God, than to have the temporary enjoyment of sin:
26 Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa.
esteeming the reproach of Christ greater riches than the treasures in Egypt, for he looked to the recompence of reward.
27 Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani.
By faith he left Egypt, not fearing the wrath of the king: for he continued firm as seeing Him who is invisible.
28 Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar’ya’yan fari yă taɓa’ya’yan fari na Isra’ila.
By faith he observed the passover and sprinkling of the blood, that he, who destroyed the first-born of the Egyptians, might not touch them.
29 Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.
By faith they passed through the Red-sea, as by dry land, which the Egyptians attempting to do were drowned.
30 Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.
By faith the walls of Jericho fell down, after they had been encompassed seven days.
31 Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci’yan leƙan asiri.
By faith Rahab the harlot perished not with the unbelievers, having received the spies with peace.
32 Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa,
And what need I say more? for the time would fail me to tell of Gideon, and Barak, and Sampson, and Jephthah, and David, and Samuel, and of the prophets:
33 waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki,
who by faith subdued kingdoms, worked righteousness, obtained promises, stopped the mouths of lions,
34 suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe.
quenched the violence of fire, escaped the edge of the sword, from weakness were made powerful, became strong in battle, and turned to flight the armies of their enemies.
35 Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu.
Women received their dead raised to life again; and others were tortured to death, not accepting deliverance, that they might obtain a better resurrection.
36 Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku.
And others had the trial of mockings and scourgings, and of bonds too and imprisonment.
37 Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci
They were stoned, they were sawn asunder, were tempted, were slain by the sword: they went about in sheep-skins, and goat-skins, being destitute, afflicted,
38 duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.
distressed, (of whom the world was not worthy) wandering in deserts, and mountains, and dens, and caves of the earth.
39 Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari.
And these all, though they obtained an honorable testimony by faith, yet received not the promise;
40 Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.
God having provided something better concerning us, that without us they might not be made perfect.

< Ibraniyawa 11 >