< Yaƙub 1 >
1 Yaƙub, bawan Allah da kuma na Ubangiji Yesu Kiristi, Zuwa ga kabilan nan goma sha biyu, da suke warwartse a cikin al’ummai. Gaisuwa mai yawa.
James a servant of God and of the Lord Jesus Christ, to the twelve tribes in dispersion sendeth greeting.
2 Ku ɗauki wannan da farin ciki mai tsabta,’yan’uwana, duk sa’ad da gwaje-gwaje na kowane iri suka zo muku,
Account it all joy, my brethren, when ye fall into various trials:
3 domin kun san cewa gwajin bangaskiyarku yakan haifi daurewa.
knowing this, that the trial of your faith worketh patience;
4 Dole daurewa ta kammala aikinta don ku zama balagaggu da kuma cikakku, ba ku kuma rasa kome ba.
but let patience have it's perfect work, that ye may be entirely perfect, failing in nothing.
5 In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi.
And if any of you lack wisdom, let him ask it of God, who giveth to all men liberally and upbraideth not, and it shall be given him.
6 Amma sa’ad da ya roƙa, dole yă gaskata, ba tare da shakka ba, domin shi mai shakka, yana kama da raƙumar ruwan tekun da iska take kori tana kuma ɓuɓɓugowa.
But let him ask in faith, nothing doubting; for he that doubteth is like a wave of the sea blown about and tossed by the wind.
7 Kada irin wannan mutum yă yi tsammani zai sami wani abu daga Ubangiji;
Let not that man think that he shall receive any thing from the Lord.
8 shi mai zuciya biyu ne, marar tsai da zuciyarsa wuri ɗaya a cikin duk abin da yake yi.
A double-minded man is inconstant in all his ways.
9 Bari ɗan’uwan da yake cikin halin ƙasƙanci yă yi taƙama a matsayinsa na ɗaukaka.
Let the brother that is low rejoice in his exaltation: but the rich in his humiliation,
10 Amma wanda yake mai arziki, ya kamata yă yi taƙama a matsayinsa na ƙasƙanci, gama ba zai daɗe ba kamar furen jeji.
because as the flower of the grass he shall pass away.
11 Gama in rana ta fito ta yi zafi mai tsanani sai ta sa tsiro yă yanƙwane tsiro; furensa yă kakkaɓe, kyansa kuma yă lalace. Haka ma mai arziki zai shuɗe yayinda yake cikin harkarsa.
For when the sun is risen with it's sultry heat, it drieth up the grass, and the flower of, it falleth, and the beauty of it's appearance is lost: so shall the rich man fade away in his projects.
12 Mai albarka ne mutumin da yake daurewa cikin gwaji, gama bayan ya yi nasara da gwajin, zai sami rawanin rai wanda Allah ya yi alkawari ga waɗanda suke ƙaunarsa.
Happy is the man who sustaineth temptation; for being approved he shall receive the crown of life, which the Lord hath promised to them that love Him.
13 Sa’ad da aka jarrabci mutum, kada yă ce, “Allah ne yake jarrabtarsa.” Gama ba ya yiwuwa a jarrabci Allah da mugunta, shi kuma ba ya jarrabtar kowa;
Let no one that is tempted say, I am tempted of God: for God cannot be tempted by evils, and He tempteth no one.
14 amma akan jarrabce kowane mutum sa’ad da muguwar sha’awarsa ta janye shi ta kuma rinjaye shi.
But every man is tempted, when drawn aside and insnared by his own vehement desire.
15 Sa’an nan, bayan da sha’awar ta yi ciki, takan haifi zunubi; zunubi kuwa, sa’ad da ya balaga yakan haifi mutuwa.
Then desire having conceived bringeth forth sin, and sin when it is finished bringeth forth death.
16 Kada a ruɗe ku,’yan’uwana ƙaunatattu.
Be not therefore deceived, my beloved brethren: for every good gift,
17 Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau.
and every perfect gift, but no evil one, is from above, and cometh down from the Father of lights, with whom there is no variation, nor shadow of turning:
18 Ya zaɓa yă haife mu ta wurin kalmar gaskiya, domin mu zama’ya’yan fari na dukan abin da ya halitta.
who hath of his own will begotten us by the word of truth, that we might be a kind of first-fruits of his creatures.
19 ’Yan’uwana ƙaunatattu, ku lura da wannan. Ya kamata kowa yă kasance mai saurin saurara, ba mai saurin magana ba, ba kuma mai saurin fushi ba,
Wherefore, my beloved brethren, let every man be swift to hear, slow to speak, slow to wrath:
20 gama fushin mutum ba ya kawo rayuwar adalcin da Allah yake so.
for the wrath of man doth not practise the righteousness of God.
21 Saboda haka, ku rabu da ƙazamin hali da kuma kowace irin mugunta ku kuma yi na’am da maganar da aka shuka a cikinku da tawali’u, wadda za tă iya cetonku.
Laying aside therefore all filthiness, and excess of malice, receive with meekness the implanted word, which is able to save your souls.
22 Kada ku zama masu ji kawai, ku ruɗi kanku. A maimakon haka ku zama masu yin abin da ta ce.
But be doers of the word, and not hearers only, deceiving yourselves.
23 Duk wanda yake ji magana ne kawai, bai kuwa aikata abin da ta ce ba, yana kama da mutumin da ya kalli fuskarsa a madubi
For if any be a hearer of the word, and not a doer, he is like a man beholding his natural face in a mirror,
24 bayan ya kalli kansa, sa’ad da ya tashi daga wurin, nan da nan sai yă manta da kamanninsa.
who beheld himself, and went away, and immediately forgot what manner of man he was.
25 Amma duk mai duba cikakkiyar ƙa’idan nan ta’yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai yă mance ba, sai dai mai yi ne yă zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake yi.
But he that looketh well into the perfect law of liberty, and continueth therein, being not a forgetful hearer, but a doer of the work, this man shall be blessed in his deed.
26 In wani ya ɗauki kansa mai addini ne duk da haka bai ƙame harshensa ba, ruɗin kansa yake yi addininsa kuwa banza ne.
If any among you seem to be religious, and bridleth not his tongue, but deceiveth his heart, this man's devotion is vain.
27 Addinin da Allah Ubanmu ya yarda da shi a matsayin mai tsabta da kuma marar aibi shi ne, a kula da marayu da gwauraye cikin damuwoyinsu, a kuma kiyaye kai daga lalacin da duniya take sa wa.
Pure and uncorrupt religion before God and our Father is this, to take care of orphans and widows in their affliction, and to keep himself unspotted from the world.