< Ibraniyawa 1 >
1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
God spoke to our fathers long ago at many times and in many ways through the prophets, but in these last days he has spoken to us through his Son,
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn )
whom he appointed heir of all things, and through whom he made the universe. (aiōn )
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
He is the radiance of God's glory and the exact representation of his nature, sustaining all things by his powerful word. When he had made purification for our sins by giving his own life, he sat down at the right hand of the Majesty in high places,
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
having become as much superior to the angels as the name he has inherited is more excellent than theirs.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
For to which of the angels did God ever say, “Yoʋ are my Son; today I have begotten yoʋ”? Or again, “I will be his Father, and he will be my Son”?
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
And again, when he brings his firstborn into the world, he says, “Let all the angels of God worship him.”
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
Of the angels he says, “He makes his angels winds, and his servants a flame of fire,”
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn )
but of the Son he says, “Yoʋr throne, O God, endures forever and ever; the scepter of yoʋr kingdom is a scepter of uprightness. (aiōn )
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
Yoʋ have loved righteousness and hated lawlessness; therefore God, yoʋr God, has anointed yoʋ with the oil of gladness beyond yoʋr companions.”
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
And, “In the beginning yoʋ, O Lord, laid the foundation of the earth, and the heavens are the works of yoʋr hands.
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
They will perish, but yoʋ remain; they will all wear out like a garment.
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
Yoʋ will roll them up like a robe, and they will be changed. But yoʋ remain the same, and yoʋr years will never come to an end.”
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
To which of the angels did God ever say, “Sit at my right hand until I make yoʋr enemies a footstool for yoʋr feet”?
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
Are they not all ministering spirits sent out to serve those who will inherit salvation?