< Ibraniyawa 1 >
1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
IN many ways, and many forms, God anciently conversed with our fathers, by the prophets:
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn )
But in these latter days, he hath conversed with us, by his Son; whom he hath constituted heir of all things, and by whom he made the worlds; (aiōn )
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
who is the splendor of his glory, and the image of himself, and upholdeth all by the energy of his word; and by himself he made a purgation of sins, and sat down on the right hand of the Majesty on high.
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
And he is altogether superior to the angels, as he hath also inherited a name which excelleth theirs.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
For to which of the angels did God ever say, Thou art my SON, this day have I begotten thee? And again, I will be to him a Father, and he shall be to me a Son?
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
And again, when bringing the first begotten into the world, he said: Let all the angels of God worship him.
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
But of the angels he thus said: Who made his angels a wind, and his ministers a flaming fire.
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn )
But of the Son he said: Thy throne, O God, is for ever and ever; a righteous sceptre is the sceptre of thy kingdom. (aiōn )
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
Thou hast loved rectitude, and hated iniquity; therefore God, thy God, hath anointed thee with the oil of gladness more than thy associates.
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
And again, Thou hast from the beginning laid the foundations of the earth, and the heavens are the work of thy hands:
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
they will pass away, but thou endurest; and they all, like a robe, wax old;
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
and like a cloak, thou wilt fold them up. They will be changed; but thou wilt be as thou art, and thy years will not be finished.
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
And to which of the angels did he ever say: Sit thou at my right hand, until I shall place thy enemies a footstool under thy feet?
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
Are they not all spirits of ministration, who are sent to minister on account of them that are to inherit life?