< Habakkuk 1 >
1 Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
The prophecy which was revealed to the prophet Habakkuk.
2 Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
How long, O Jehovah, do I cry, and thou dost not hear! How long do I complain to thee of violence, and thou dost not save!
3 Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
Why dost thou suffer me to see iniquity, And why dost thou look upon wickedness? For spoiling and violence are before me; There is contention, and strife exalteth itself.
4 Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
Therefore the law faileth, And judgment is not pronounced according to truth; For the wicked encompasseth the righteous, Therefore wrong judgment is pronounced.
5 “Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
Behold ye among the nations, and look! Yea, wonder, and be astonished! For I do a work in your days Which ye will not believe though it be told you.
6 Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
For behold, I raise up the Chaldeans, A fierce and swift people, Which go over the breadth of the earth, To take possession of dwelling-places that are not their own.
7 Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
They are terrible and dreadful; From themselves go forth their law and their dignity.
8 Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
Their horses are swifter than leopards, And fiercer than evening wolves. Their horsemen leap proudly; Their horsemen come from far; They fly like an eagle, hastening to devour.
9 duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
All of them come for violence; The multitude of their faces is directed forwards, And they gather captives as sand.
10 Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
They also scoff at kings, And princes are to them a laughing-stock; They deride every stronghold, For they heap up earth and take it.
11 Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
Then their spirit is uplifted, and they transgress, and become guilty; This their strength is made their god.
12 Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
Art thou not from everlasting, O Jehovah, my God, my Holy One? We shall not die! Thou, O Jehovah, hast appointed them for judgment; Thou, O Rock, hast ordained them for chastisement.
13 Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
Thou art of purer eyes than to behold evil, And canst not look on wickedness; Why then dost thou look on transgressors, And art silent, when the wicked swalloweth up the man that is more righteous than he?
14 Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
And why makest thou men as the fishes of the sea, As the reptiles that have no ruler?
15 Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
They take up all of them with the hook, They catch them in their net, And gather them in their drag; Therefore they rejoice and exult.
16 Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
Therefore they sacrifice to their net, And burn incense to their drag; Because by them their portion is fat, And their food plenteous.
17 Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?
Shall they therefore empty the net, And slay the nations continually without mercy?