< Zefaniya 1 >
1 Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
The word of Jehovah, which came to Zephaniah, the son of Cushi, the son of Gedaliah, the son of Amariah, the son of Hizkiah, in the days of Josiah, the son of Amon, king of Judah.
2 “Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
I will utterly consume all things from the face of the land, saith Jehovah;
3 “Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
I will consume man and beast; I will consume the birds of heaven, and the fishes of the sea, And the stumbling-blocks with the wicked; And I will cut off man from the face of the land, saith Jehovah.
4 “Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
I will stretch out my hand over Judah, And over all the inhabitants of Jerusalem, And I will cut off from this place the residue of Baal, The name of the idol-sacrificers with the priests,
5 waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
And those who bow themselves on the house-tops to the host of heaven, And those who bow themselves and swear by Jehovah, And also swear by their idol,
6 Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
And those that turn back from Jehovah, And those that seek not Jehovah, nor inquire for him.
7 Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
Be silent before the Lord Jehovah! For the day of Jehovah is near; For Jehovah hath prepared a sacrifice; He hath appointed his guests.
8 “A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
And in the day of the sacrifice of Jehovah it shall come to pass That I will punish the princes and the sons of the king, And all that are clothed with foreign apparel.
9 A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
In that day also will I punish all that leap over the threshold, That fill the houses of their master with violence and deceit.
10 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
And it shall come to pass in that day, saith Jehovah, That there shall be the noise of a cry from the fish-gate, And of a howling from the other part of the city, And of great destruction from the hills.
11 Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
Howl, ye inhabitants of Maktesh! For all the trafficking people are cut down; All they that bear silver are destroyed.
12 A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
And it shall come to pass at that time, That I will search Jerusalem with lamps, And I will punish the men that are settled on their lees; That say in their hearts, “Jehovah doeth neither good nor evil.”
13 Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
Their substance shall become a spoil, And their houses a desolation; They shall also build houses, but not inhabit them; And shall plant vineyards, but not drink the wine thereof.
14 Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
The day of Jehovah is near, the great day; It is near, and hasteth greatly; The day of Jehovah shall resound; Bitterly shall the mighty man cry for help.
15 Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
That day is a day of wrath, A day of distress and anguish, A day of destruction and desolation, A day of darkness and gloominess, A day of clouds and thick darkness,
16 rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
A day of the trumpet and the war-shout, Against the fenced cities, And against the high towers.
17 “Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
And I will distress the men, so that they shall walk like the blind, Because they have sinned against Jehovah. And their blood shall be poured out as dust, And their flesh as dung.
18 Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.
Neither their silver nor their gold shall be able to deliver them in the day of the wrath of Jehovah, But by the fire of his indignation shall the whole land be devoured; For destruction, and that a speedy one, will he bring Upon all that dwell in the land.