< Farawa 10 >
1 Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
Voici la postérité des fils de Noé, Sem, Cham et Japhet. Il leur naquit des fils après le déluge.
2 ’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
Les fils de Japhet furent: Gomer, Magog, Madaï, Javan, Tubal, Méschec et Tiras.
3 ’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
Les fils de Gomer: Aschkenaz, Riphat et Togarma.
4 ’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
Les fils de Javan: Élischa, Tarsis, Kittim et Dodanim.
5 (Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
C’est par eux qu’ont été peuplées les îles des nations selon leurs terres, selon la langue de chacun, selon leurs familles, selon leurs nations.
6 ’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
Les fils de Cham furent: Cusch, Mitsraïm, Puth et Canaan.
7 ’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
Les fils de Cusch: Saba, Havila, Sabta, Raema et Sabteca. Les fils de Raema: Séba et Dedan.
8 Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
Cusch engendra aussi Nimrod; c’est lui qui commença à être puissant sur la terre.
9 Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
Il fut un vaillant chasseur devant l’Éternel; c’est pourquoi l’on dit: Comme Nimrod, vaillant chasseur devant l’Éternel.
10 Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
Il régna d’abord sur Babel, Érec, Accad et Calné, au pays de Schinear.
11 Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
De ce pays-là sortit Assur; il bâtit Ninive, Rehoboth Hir, Calach,
12 da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
et Résen entre Ninive et Calach; c’est la grande ville.
13 Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
Mitsraïm engendra les Ludim, les Anamim, les Lehabim, les Naphtuhim,
14 Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
les Patrusim, les Casluhim, d’où sont sortis les Philistins, et les Caphtorim.
15 Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
Canaan engendra Sidon, son premier-né, et Heth;
16 Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
et les Jébusiens, les Amoréens, les Guirgasiens,
17 Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
les Héviens, les Arkiens, les Siniens,
18 Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
les Arvadiens, les Tsemariens, les Hamathiens. Ensuite, les familles des Cananéens se dispersèrent.
19 har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
Les limites des Cananéens allèrent depuis Sidon, du côté de Guérar, jusqu’à Gaza, et du côté de Sodome, de Gomorrhe, d’Adma et de Tseboïm, jusqu’à Léscha.
20 Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
Ce sont là les fils de Cham, selon leurs familles, selon leurs langues, selon leurs pays, selon leurs nations.
21 Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
Il naquit aussi des fils à Sem, père de tous les fils d’Héber, et frère de Japhet l’aîné.
22 ’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
Les fils de Sem furent: Élam, Assur, Arpacschad, Lud et Aram.
23 ’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
Les fils d’Aram: Uts, Hul, Guéter et Masch.
24 Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
Arpacschad engendra Schélach; et Schélach engendra Héber.
25 Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
Il naquit à Héber deux fils: le nom de l’un était Péleg, parce que de son temps la terre fut partagée, et le nom de son frère était Jokthan.
26 Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
Jokthan engendra Almodad, Schéleph, Hatsarmaveth, Jérach,
28 Obal, Abimayel, Sheba,
Obal, Abimaël, Séba,
29 Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
Ophir, Havila et Jobab. Tous ceux-là furent fils de Jokthan.
30 Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
Ils habitèrent depuis Méscha, du côté de Sephar, jusqu’à la montagne de l’orient.
31 Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
Ce sont là les fils de Sem, selon leurs familles, selon leurs langues, selon leurs pays, selon leurs nations.
32 Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.
Telles sont les familles des fils de Noé, selon leurs générations, selon leurs nations. Et c’est d’eux que sont sorties les nations qui se sont répandues sur la terre après le déluge.