< Farawa 10 >

1 Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
(This is/I will now give) a list of the descendants of Noah’s sons, Shem, Ham, and Japheth. They had many children after the flood.
2 ’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
The sons of Japheth were Gomer, Magog, Madai, Javan, Tubal, Meshech, and Tiras.
3 ’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
The sons of Gomer were Askenaz, Riphath, and Togarmah.
4 ’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
The sons of Javan were Elishah, Tarshish, Kittim, and Dodanim.
5 (Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
Those sons and their families who were descended from Javan lived on the islands and on the land close to the [Mediterranean] Sea. Their descendants became tribes, each with its own language and clans and territory.
6 ’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
The descendants of Ham were Cush, Egypt, Put, and Canaan.
7 ’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
The descendants of Cush were Seba, Havilah, Sabtah, Raamah, and Sabteca. The descendants of Raamah were Sheba and Dedan.
8 Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
Another one of Cush’s descendants was Nimrod. Nimrod was the first person on earth who became a mighty warrior.
9 Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
Yahweh saw that he had become (OR, caused him to become) a great hunter. That is why people say to a great hunter, “Yahweh (sees that you are/has caused you to be) a great hunter like Nimrod.”
10 Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
Nimrod became a king who ruled in Babylonia. The first cities over which he ruled were Babel, Erech, Accad, and Calneh.
11 Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
From there he went [with others] to Assyria and built the cities of Nineveh, Rehoboth-Ir, Calah,
12 da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
and Resen. Resen was a large city between Nineveh and Calah.
13 Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
Ham’s son, Egypt, became the ancestor of the Lud, Anam, Lehab and Naphtuh,
14 Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
Pathrus, Casluh and Caphtor people-groups. The Philistine people were descended from Casluh.
15 Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
Ham’s youngest son, Canaan, became the father of Sidon, who was his eldest son, and Heth, his younger son.
16 Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
Canaan was also the ancestor of the Jebus, Amor, Girgash,
17 Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
Hiv, Ark, Sin,
18 Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
Arved, Zemar and Hamath people-groups. Later the descendants of Canaan dispersed over a large area.
19 har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
Their land extended from Sidon [city] in the north as far south as Gaza [town], and then to the east as far as Gerar [town], and then farther east to Sodom, Gomorrah, Admah, and Zeboiim [towns], and even as far as Lasha [town].
20 Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
Those are the descendants of Ham. They became groups that had their own clans, their own languages, and their own land.
21 Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
Shem, the older brother of Japheth, became the father of Eber, and the ancestor of all the descendants of Eber.
22 ’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
The sons of Shem were Elam, Asshur, Arphaxad, Lud, and Aram.
23 ’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
The sons of Aram were Uz, Hul, Gether, and Mash.
24 Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
Arphaxad became the father of Shelah. Shelah became the father of Eber.
25 Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
Eber became the father of two sons. One of them was named Peleg, [which means ‘division’], because during the time he lived, people on [MTY] the earth became divided and scattered everywhere. Peleg’s younger brother was Joktan.
26 Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
Joktan became the ancestor of Almodad, Sheleph, Hazarmaveth, Jerah,
27 Hadoram, Uzal, Dikla,
Hadoram, Uzal, Diklah,
28 Obal, Abimayel, Sheba,
Obal, Abimael, Sheba,
29 Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
Ophir, Havilah, and Jobab. All those people were descended from Joktan.
30 Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
The areas in which they lived extended from Mesha westward to Sephar, which is in the (hill country/area that has a lot of hills).
31 Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
They are descendants of Shem. They became groups that had their own clans, their own languages, and their own land.
32 Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.
All those groups descended from the sons of Noah. Each group had its own (genealogy/record of people’s ancestors) and each became a separate ethnic group. Those ethnic groups formed after the flood and spread all around the earth.

< Farawa 10 >