< Farawa 10 >

1 Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
Now these [are] the generations of the sons of Noe, Sem, Cham, Japheth; and sons were born to them after the flood.
2 ’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
The sons of Japheth, Gamer, and Magog, and Madoi, and Jovan, and Elisa, and Thobel, and Mosoch, and Thiras.
3 ’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
And the sons of Gamer, Aschanaz, and Riphath, and Thorgama.
4 ’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
And the sons of Jovan, Elisa, and Tharseis, Cetians, Rhodians.
5 (Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
From these were the islands of the Gentiles divided in their land, each according to his tongue, in their tribes and in their nations.
6 ’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
And the sons of Cham, Chus, and Mesrain, Phud, and Chanaan.
7 ’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
And the sons of Chus, Saba, and Evila, and Sabatha, and Rhegma, and Sabathaca. And the sons of Rhegma, Saba, and Dadan.
8 Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
And Chus begot Nebrod: he began to be a giant upon the earth.
9 Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
He was a giant hunter before the Lord God; therefore they say, As Nebrod the giant hunter before the Lord.
10 Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
And the beginning of his kingdom was Babylon, and Orech, and Archad, and Chalanne, in the land of Senaar.
11 Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
Out of that land came Assur, and built Ninevi, and the city Rhooboth, and Chalach,
12 da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
and Dase between Ninevi and Chalach: this is the great city.
13 Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
And Mesrain begot the Ludiim, and the Nephthalim, and the Enemetiim, and the Labiim,
14 Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
and the Patrosoniim, and the Chasmoniim (whence came forth Phylistiim) and the Gaphthoriim.
15 Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
And Chanaan begot Sidon his firstborn, and the Chettite,
16 Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
and the Jebusite, and the Amorite, and the Girgashite,
17 Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
and the Evite, and the Arukite, and the Asennite,
18 Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
and the Aradian, and the Samarean, and the Amathite; and after this the tribes of the Chananites were dispersed.
19 har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
And the boundaries of the Chananites were from Sidon till one comes to Gerara and Gaza, till one comes to Sodom and Gomorrha, Adama and Seboim, as far as Dasa.
20 Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
There [were] the sons of Cham in their tribes according to their tongues, in their countries, and in their nations.
21 Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
And to Sem himself also were children born, the father of all the sons of Heber, the brother of Japheth the elder.
22 ’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
Sons of Sem, Elam, and Assur, and Arphaxad, and Lud, and Aram, and Cainan.
23 ’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
And sons of Aram, Uz, and Ul, and Gater, and Mosoch.
24 Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
And Arphaxad begot Cainan, and Cainan begot Sala. And Sala begot Heber.
25 Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
And to Heber were born two sons, the name of the one, Phaleg, because in his days the earth was divided, and the name of his brother Jektan.
26 Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
And Jektan begot Elmodad, and Saleth, and Sarmoth, and Jarach,
27 Hadoram, Uzal, Dikla,
and Odorrha, and Aibel, and Decla,
28 Obal, Abimayel, Sheba,
Eval, and Abimael, and Saba,
29 Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
and Uphir, and Evila, and Jobab, all these were the sons of Jektan.
30 Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
And their dwelling was from Masse, till one comes to Saphera, a mountain of the east.
31 Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
These were the sons of Sem in their tribes, according to their tongues, in their countries, and in their nations.
32 Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.
These are the tribes of the sons of Noe, according to their generations, according to their nations: of them were the islands of the Gentiles scattered over the earth after the flood.

< Farawa 10 >