< Ezekiyel 29 >
1 A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La dixième année, au dixième mois, le douzième jour du mois, la parole de l'Éternel me fut adressée en ces termes:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
« Fils d'homme, tourne ta face vers Pharaon, roi d'Égypte, et prophétise contre lui et contre toute l'Égypte.
3 Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
Parle et dis: Le Seigneur Yahvé dit: « Voici, je suis contre toi, Pharaon, roi d'Égypte, le grand monstre qui se trouve au milieu de ses rivières, qui a dit: « Mon fleuve est à moi », et je l'ai fait pour moi.
4 Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
Je mettrai des crochets dans vos mâchoires, et je ferai en sorte que les poissons de vos rivières se collent à vos écailles. Je vous ferai sortir du milieu de vos rivières, avec tous les poissons de vos rivières qui s'accrochent à vos écailles.
5 Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
Je te jetterai dans le désert, vous et tous les poissons de vos rivières. Tu vas tomber sur le champ libre. Vous ne serez pas réunis ou rassemblés. Je vous ai donné en nourriture aux animaux de la terre. et aux oiseaux du ciel.
6 Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
"''Tous les habitants de l'Égypte sauront que je suis Yahvé, parce qu'ils ont été un bâton de roseau pour la maison d'Israël.
7 Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
Quand ils t'ont saisi par la main, tu as brisé et déchiré toutes leurs épaules. Quand ils se sont appuyés sur toi, tu as brisé et paralysé toutes leurs cuisses. »
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
"'C'est pourquoi le Seigneur Yahvé dit: « Voici que je fais venir sur vous l'épée, et j'extermine de vous hommes et bêtes.
9 Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
Le pays d'Égypte sera une désolation et un désert. Alors ils sauront que je suis Yahvé. "" Parce qu'il a dit: Le fleuve est à moi, et c'est moi qui l'ai fait »,
10 saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
voici que j'en veux à toi et à tes fleuves. Je ferai du pays d'Égypte un désert et une désolation totale, depuis la tour de Seveneh jusqu'à la frontière de l'Éthiopie.
11 Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
Aucun pied d'homme n'y passera, aucun pied d'animal n'y passera. Il ne sera pas habité pendant quarante ans.
12 Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
Je ferai du pays d'Égypte une désolation au milieu des pays qui sont désolés. Ses villes au milieu des villes dévastées seront une désolation pendant quarante ans. Je disperserai les Égyptiens parmi les nations, je les disperserai à travers les pays. »
13 “‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
"'Car le Seigneur Yahvé dit: « Au bout de quarante ans, je rassemblerai les Égyptiens des peuples où ils ont été dispersés.
14 Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
Je renverserai la captivité de l'Égypte et je les ferai retourner dans le pays de Pathros, dans le pays de leur naissance. Là, ils formeront un royaume modeste.
15 Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
Il sera le plus bas des royaumes. Il ne s'élèvera plus au-dessus des nations. Je les diminuerai au point qu'ils ne domineront plus sur les nations.
16 Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Il ne sera plus l'assurance de la maison d'Israël, rappelant l'iniquité, quand on se tourne vers lui. Alors ils sauront que je suis le Seigneur Yahvé. »'"
17 A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La vingt-septième année, le premier jour du mois, la parole de l'Éternel me fut adressée, en ces mots:
18 “Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
« Fils d'homme, Nebucadnetsar, roi de Babylone, a fait faire à son armée un grand service contre Tyr. Toutes les têtes étaient chauves, et toutes les épaules étaient usées; mais il n'a pas reçu de salaire, ni son armée de Tyr, pour le service qu'il a fait contre elle.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
C'est pourquoi le Seigneur Yahvé dit: « Voici que je donne le pays d'Égypte à Nabuchodonosor, roi de Babylone. Il enlèvera sa multitude, prendra son pillage et son butin. Ce sera le salaire de son armée.
20 Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Je lui ai donné le pays d'Égypte en paiement de son service, parce qu'ils ont travaillé pour moi, dit le Seigneur Yahvé.
21 “A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
« En ce jour-là, je ferai germer une corne pour la maison d'Israël, et j'ouvrirai ta bouche au milieu d'eux. Alors ils sauront que je suis Yahvé. »