< Daniyel 1 >
1 A Shekara ta uku ta mulki Yehohiyakim sarkin Yahuda, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zo Urushalima ya kuma yi mata ƙawanya.
La troisième année du règne de Jojakim, roi de Juda, Nebucadnetsar, roi de Babylone, vint à Jérusalem et l'assiégea.
2 Sai Ubangiji ya bashe Yehohiyakim sarkin Yahuda a hannunsa, tare da waɗansu kayayyakin haikalin Allah. Ya ɗauki waɗannan kayan zuwa cikin haikalin allahnsa a Babilon cikin ma’ajin gidan allahnsa.
L'Éternel livra entre ses mains Jehoïakim, roi de Juda, avec une partie des ustensiles de la maison de Dieu, et il les transporta au pays de Schinear, dans la maison de son dieu. Il apporta les ustensiles dans la maison du trésor de son dieu.
3 Sa’an nan sarkin ya umarci Ashfenaz, shugaban fadarsa yă kawo waɗansu daga cikin Isra’ilawan da suka fito daga gidan sarauta da kuma na fitattun mutane.
Le roi parla à Ashpenaz, maître de ses eunuques, pour qu'il fasse venir quelques-uns des enfants d'Israël, de la descendance royale et des nobles:
4 Matasa maza waɗanda ba su da wata naƙasa kuma kyawawa, hazikai ta kowace hanyar koyo, sanannu, masu saurin fahimtar abu, da kuma waɗanda suka cancanci su yi aiki a fadar sarki. Zai koya musu harshen Babiloniyawa da kuma littattafansu.
des jeunes gens qui n'avaient pas de défaut, mais qui étaient de bonne constitution, habiles en toute sagesse, doués de savoir, comprenant la science, et qui étaient capables de se tenir dans le palais du roi; et qu'il leur enseignât le savoir et la langue des Chaldéens.
5 Sarki kuma ya sa a ba su abinci da ruwan inabi kowace rana daga cikin abincin sarki. Za a koyar da su har shekaru uku, bayan haka kuma su shiga yin wa sarki hidima.
Le roi leur donna une portion quotidienne des mets du roi et du vin qu'il buvait, et leur imposa une nourriture de trois ans, à l'issue de laquelle ils se présenteraient devant le roi.
6 Daga cikin waɗannan da aka zaɓa akwai waɗansu daga Yahuda, Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya.
Or, parmi ces enfants de Juda, il y avait Daniel, Hanania, Mishaël et Azaria.
7 Sai sarkin fada ya raɗa musu sababbin sunaye, ga Daniyel ya raɗa masa Belteshazar; ga Hananiya ya raɗa masa Shadrak; ga Mishayel ya raɗa masa Meshak; ga Azariya kuma ya raɗa masa Abednego.
Le prince des eunuques leur donna des noms: à Daniel, il donna le nom de Beltschatsar; à Hanania, celui de Shadrac; à Mishael, celui de Meshach; et à Azaria, celui d'Abednego.
8 Amma Daniyel ya ƙudura a zuciyarsa ba zai ƙazantar da kansa da abinci da ruwan inabin sarki ba, sai ya tambayi sarkin fada don a ba shi izinin kada yă ƙazantar da kansa ta wannan hanya.
Mais Daniel résolut dans son cœur de ne pas se souiller avec les mets du roi et avec le vin qu'il buvait. Il demanda donc au prince des eunuques de ne pas se souiller.
9 Sai Allah ya sa sarkin fada ya nuna masa tagomashi ya kuma ƙaunaci Daniyel,
Dieu fit en sorte que Daniel trouve de la bonté et de la compassion aux yeux du prince des eunuques.
10 amma sai sarkin fada ya ce wa Daniyel, “Ina jin tsoron ranka yă daɗe, sarkina wanda ya sa a ba ku abinci da ruwan inabi. Me zai sa yă ga kuna ramewa fiye da sauran samari, tsaranku? Sarki zai sa a fille mini kai saboda ku.”
Le prince des eunuques dit à Daniel: « Je crains mon seigneur le roi, qui a fixé votre nourriture et votre boisson. Car pourquoi verrait-il vos visages plus mauvais que ceux des jeunes gens de votre âge? Vous mettriez alors ma tête en danger auprès du roi. »
11 Sai Daniyel ya ce wa mai gadi wanda sarkin fada ya sa yă kula da Daniyel, Hananiya, Mishayel da Azariya,
Alors Daniel dit à l'intendant que le prince des eunuques avait nommé sur Daniel, Hanania, Mischaël et Azaria:
12 “Ina roƙonka ka gwada bayinka kwana goma. Kada ka ba mu kome sai kayan lambu mu ci da kuma baƙin ruwa mu sha.
« Mets tes serviteurs à l'épreuve, je t'en prie, pendant dix jours; qu'ils nous donnent des légumes à manger et de l'eau à boire.
13 Sa’an nan sai ka dubi fuskokinmu da na sauran samarin da suke ci daga abincin sarki; sa’an nan ka yi da bayinka bisa ga abin da ka gani.”
Puis, que l'on examine devant toi notre visage et celui des jeunes gens qui mangent les mets du roi; et selon ce que tu verras, traite tes serviteurs. »
14 Sai ya amince da haka ya kuma gwada su har kwana goma.
Il les écouta donc à ce sujet et les mit à l'épreuve pendant dix jours.
15 A ƙarshen kwana goma sai aka ga fuskokinsu suna sheƙi, sun kuma yi ƙiba fiye da samarin da suke cin abinci irin na sarki.
Au bout de dix jours, leur visage était plus beau et ils étaient plus gras que tous les jeunes gens qui avaient mangé les mets du roi.
16 Sai mai gadinsu ya janye abinci da ruwan inabi irin na sarki, ya ci gaba da ba su kayan lambu.
L'intendant enleva leurs mets et le vin qu'on leur avait donné à boire, et leur donna des légumes.
17 Ga samarin nan guda huɗu Allah ya ba su sani da ganewar dukan irin littattafai da kuma koyarwa. Daniyel kuma ya iya gane wahayi da kowane irin mafarki.
Quant à ces quatre jeunes gens, Dieu leur donna de la connaissance et de l'habileté dans toute l'instruction et la sagesse; et Daniel eut l'intelligence de toutes les visions et de tous les songes.
18 A ƙarshen lokacin da sarki ya sa da za a kawo su ciki, sai sarkin fada ya gabatar da su ga Nebukadnezzar.
A la fin des jours que le roi avait fixés pour les faire venir, le prince des eunuques les fit venir devant Nebucadnetsar.
19 Sarki kuwa ya yi magana da su, sai ya gano cewa babu wani kamar Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya; don haka sai suka shiga yi wa sarki hidima.
Le roi s'entretint avec eux, et il ne se trouva parmi eux personne comme Daniel, Hanania, Mishaël et Azaria. Ils se tinrent donc devant le roi.
20 A dukan al’amuran hikima da na fahimta wanda sarki ya tambaye su, ya tarar sun fi dukan masu sihiri da bokaye waɗanda suke cikin mulkinsa sau goma.
Pour toutes les questions de sagesse et d'intelligence que le roi leur posa, il les trouva dix fois meilleurs que tous les magiciens et enchanteurs qui étaient dans tout son royaume.
21 Daniyel kuwa ya kasance a nan har shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus.
Daniel a continué jusqu'à la première année du roi Cyrus.