< Ezekiyel 26 >
1 A shekara ta goma sha ɗaya, a rana ta fari ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
II arriva dans la onzième année, le premier du mois, que la parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
2 “Ɗan mutum, domin Taya ta yi magana a kan Urushalima ta ce, ‘Yauwa! Ƙofar zuwa al’ummai ta karye, an kuma buɗe mini ƙofofinta; yanzu da take kufai zan wadace,’
"Fils de l’homme, parce que Tyr s’est écriée au sujet de Jérusalem: Ah! Elle est brisée, celle qui était la porte des nations! Mon tour est venu: je vais être comblée, puisqu’elle est ruinée,
3 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da ke, ya Taya, zan kuwa kawo al’ummai masu yawa su yi gāba da ke, kamar yadda teku takan kawo raƙuman ruwa.
c’est pourquoi, ainsi parle le Seigneur Dieu: Voici que je m’en prends à toi, Tyr; je soulèverai contre toi des nations nombreuses comme la mer soulève ses vagues.
4 Za su hallaka katangar Taya su kuma rurrushe hasumiyoyinta; zan kankare tarkacenta, in maishe ta fā.
Elles détruiront les remparts de Tyr et démoliront ses tours; je la dénuderai de sa poussière et je ferai d’elle une roche aride.
5 Za tă zama wurin shanya abin kamun kifi a tsakiyar teku, gama na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Za tă zama ganima ga sauran al’ummai,
Elle deviendra un étendoir à filets au milieu de la mer, car c’est moi qui parle, dit le Seigneur Dieu, et elle sera une proie pour les nations.
6 za a kashe mazaunan filin ƙasar da takobi. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.
Et ses filles qui sont dans la campagne seront massacrées par le glaive; ainsi ils sauront que je suis l’Eternel.
7 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa daga arewa zan kawo wa Taya Nebukadnezzar sarkin Babilon, sarkin sarakuna, tare da dawakai da kekunan yaƙi, da mahayan dawakai da babbar rundunar soja.
Oui, ainsi parle le Seigneur Dieu, je vais, du Nord, amener contre Tyr Nabuchodonosor, roi de Babylone, le roi des rois, avec des chevaux, des chars, des cavaliers, une grande multitude et un peuple nombreux.
8 Zai kashe mazaunan filin ƙasar da takobi; zai yi miki ƙawanya, ya gina miki mahaurai, sa’an nan ya rufe ki da garkuwoyi.
Tes filles qui sont dans la campagne, il les fera périr par l’épée, et contre toi il élèvera des retranchements, jettera des redoutes et dressera des boucliers.
9 Zai rushe katangarki da dundurusai, ya rurrushe hasumiyoyinki da makamai.
Les coups de son bélier, il les assénera sur tes remparts, et tes tours, il les brisera par ses armes.
10 Dawakansa za su yi yawa har su rufe ke da ƙura. Katanga za su girgiza saboda motsin dawakan yaƙi, kekunan doki da keken yaƙin sa’ad da suka shiga birnin da aka rushe katangar.
Grâce à la multitude de ses chevaux, il te couvrira de leur poussière; du bruit des cavaliers, des roues et des chars tes murailles trembleront, quand il entrera par tes portes comme on entre dans une ville éventrée.
11 Kofatan dawakansa za su tattake dukan titunanki; zai kashe mutanenki da takobi, ginshiƙanki masu ƙarfi kuma za su fāɗi a ƙasa.
Sous les sabots de ses chevaux il foulera toutes tes rues, ta population, il la tuera par l’épée, et les monuments de ta puissance tomberont à terre.
12 Za su washe dukiyarki, kayan cinikinki kuma su zama ganima; za su rurrushe katangarki su ragargaza gidajenki masu kyau su kuma zubar da duwatsunki, katakanki da kuma tarkacenki a cikin teku.
Ils pilleront tes richesses, feront main basse sur tes marchandises; ils démoliront tes murailles et abattront tes maisons de plaisance; tes pierres, tes bois et ta poussière, ils les jetteront dans l’eau.
13 Zan kawo ƙarshen waƙoƙinki masu surutu, ba kuwa za a ƙara jin kaɗe-kaɗen garayunki ba.
Je mettrai fin à la rumeur de tes chants, et le son de tes harpes ne se fera plus entendre.
14 Zan maishe ki fā, za ki kuma zama wurin shanya abin kamun kifi. Ba za a sāke gina ki ba, gama Ni Ubangiji na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Je ferai de toi une roche aride, tu deviendras un étendoir à filets. Tu ne seras plus rebâtie, car c’est moi, l’Eternel, qui parle, dit le Seigneur Dieu."
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Taya. Ƙasashen da suke a bakin teku ba za su girgiza saboda ƙarar fāɗuwarki, sa’ad da nishin waɗanda aka yi wa rauni da kashe-kashen da aka yi a cikinki suka faru ba?
Ainsi parle le Seigneur Dieu à Tyr: "Certes, au bruit de ta chute, aux gémissements des mourants, quand s’accomplira la tuerie au milieu de toi, les îles trembleront.
16 Sa’an nan sarakunan bakin teku za su sauka daga gadajen sarautarsu, su tuɓe rigunansu, da rigunansu waɗanda aka yi wa ado. Za su zauna a ƙasa suna rawar jiki a kowane lokaci suna razana saboda abin da ya same ki.
Ils descendront de leurs trônes, tous les princes de la mer, ils ôteront leurs manteaux et dépouilleront leurs vêtements brodés; ils se vêtiront d’épouvante, s’asseoiront à terre, frissonneront à tout instant et seront atterrés à cause de toi.
17 Sa’an nan za su yi makoki game da ke su ce, “‘Yaya kika hallaka haka nan, ya birnin da ta yi suna, cike da mutanen teku! Ke da kika zama mai ƙarfi cikin tekuna, ke da mazauna cikinki; kin sa tsoronki a kan dukan waɗanda suka zauna a can.
Ils entonneront sur toi une complainte et te diront: "Comme tu as péri, toi si populeuse grâce aux mers, ville illustre, si puissante sur les flots, toi et tes habitants, qui inspiraient la terreur à tous les voisins!
18 Yanzu tsibirai suna rawar jiki a ranar fāɗuwarki; tsibirai a cikin teku sun tsorata a ɓacewarki.’
Maintenant les côtes tremblent au jour de ta chute, et les îles qui sont dans la mer sont épouvantées de ta fin.
19 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na maishe ki kufai, kamar sauran biranen da ba a ƙara zama a ciki, sa’ad da kuma na kawo zurfafan teku a kanki da yawan ruwansa suka rufe ki,
Car, ainsi parle le Seigneur Dieu, lorsque je ferai de toi une ville ruinée, pareille aux villes qui ne sont plus habitées, lorsque je soulèverai contre toi les ondes de l’abîme et que te couvriront les eaux profondes,
20 a sa’an nan zan sauko da ke ƙasa tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, zuwa wurin mutanen dā. Zan sa ki zauna ƙarƙashin ƙasa, kamar a kufai na tun dā, tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, ba kuwa za ki ƙara dawowa ba ko ki ɗauki matsayinki a ƙasar masu rai.
alors je te précipiterai avec ceux qui sont descendus dans la fosse, auprès des gens des temps antiques, et je te confinerai dans les régions souterraines, dans les ruines éternelles, auprès de ceux qui sont descendus dans la fosse, afin que tu cesses d’être habitée, tandis que je répandrai de la beauté au pays des vivants.
21 Zan sa ki yi mummunan ƙarshe kuma ba za ki ƙara kasancewa ba. Za a neme ki, amma ba za a ƙara same ki ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Je te réduirai à néant et c’en sera fini de toi: l’on te cherchera et plus jamais l’on ne te trouvera", dit le Seigneur Dieu."