< Ezekiyel 25 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
"Fils de l’homme, dirige ta face contre les fils d’Ammon, et prophétise sur eux.
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
Tu diras aux fils d’Ammon: Ecoutez la parole du Seigneur Dieu! Ainsi parle le Seigneur Dieu: Parce que tu as crié: Holà! sur mon sanctuaire, lorsqu’il fut profané, sur la terre d’Israël, lorsqu’elle fut dévastée, et sur la maison do Juda, lorsqu’elle partit pour l’exil,
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
c’est pourquoi je te livre aux fils de l’Orient en toute propriété; ils installeront leurs campements chez toi et y établiront leurs habitations; c’est eux qui mangeront tes fruits, eux qui boiront ton lait.
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Je ferai de Rabba un pacage de chameaux et des fils d’Ammon un cantonnement de brebis, et vous saurez que je suis l’Eternel."
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
"Oui, ainsi parle le Seigneur Dieu, parce que tu as battu des mains, trépigné du pied, et que tu t’es réjouie avec tant de mépris, du fond de l’âme, au sujet du pays d’Israël,
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
c’est pourquoi je vais étendre ma main sur toi et te donner en proie aux nations; je te retrancherai du rang des peuples et te ferai disparaître d’entre les pays, je te réduirai à néant, et tu sauras que je suis l’Eternel."
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
Ainsi parle le Seigneur Dieu: "Parce que Moab et Séir ont dit: Voilà que la maison de Juda est comme toutes les nations.
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
C’Est pourquoi je vais entamer le flanc de Moab, en le privant des villes, de ses villes extrêmes, la parure du pays, de Béth-Hayechimot, Baal-Meôn et Kiriataïm.
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
Aux fils de l’Orient, contre les fils d’Ammon, je donne ce district en possession, afin que les fils d’Ammon ne soient plus mentionnés parmi les peuples.
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
Et j’infligerai des châtiments à Moab et ils sauront que je suis l’Eternel."
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
Ainsi parle le Seigneur Dieu: "A cause des procédés d’Edom, quand il a tiré vengeance de la maison de Juda, et parce qu’il s’est rendu coupable par les représailles qu’il a exercées,
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
c’est pourquoi, ainsi parle le Seigneur Dieu, j’étendrai ma main sur Edom et j’en exterminerai hommes et bêtes; j’en ferai une ruine depuis Têmân, et jusqu’à Dedân ils tomberont sous l’épée.
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Je confierai le soin de ma vengeance contre Edom à la main de mon peuple Israël; ils traiteront Edom conformément à ma colère et à ma fureur, et il se ressentira de ma vengeance, dit le Seigneur Dieu."
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
Ainsi parle le Seigneur Dieu: "Parce que les Philistins ont agi par vengeance, qu’ils se sont livrés à des représailles dans un profond sentiment de mépris, cherchant à détruire dans leur éternelle haine,
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
c’est pourquoi, ainsi parle le Seigneur Dieu, voici que je vais étendre ma main sur les Philistins, anéantir les Kerêthites et faire périr ce qui reste sur le littoral de la mer.
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
J’Exercerai sur eux de grandes vengeances, par de violents sévices, et ils sauront que je suis l’Eternel, alors que je ferai éclater ma vengeance parmi eux."