< Ezekiyel 24 >
1 A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ngomnyaka wesificamunwemunye, ngenyanga yetshumi, ngosuku lwetshumi, ilizwi likaThixo lafika kimi lisithi:
2 “Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
“Ndodana yomuntu, bhala usuku lolu, usuku lolu lona ngokwalo, ngoba iNkosi yaseBhabhiloni isivimbezele iJerusalema ngalo kanye lolusuku.
3 Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
Tshela indlu le ehlamukayo umfanekiso uthi kubo: ‘Nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi: Beka imbiza yokupheka eziko; ibeke phezu kwamaseko uthele amanzi phakathi kwayo.
4 Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
Faka phakathi kwayo amaqatha enyama, wonke amaqatha amahle, umlenze lesiphanga. Igcwalise ngamathambo amahle;
5 ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
thatha okukhethiweyo emhlambini. Basela kakhulu ngenkuni usenzela amathambo; ixhwathise upheke amathambo phakathi kwayo.
6 “‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
Ngoba nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi: Maye kulo idolobho lokuchithwa kwegazi, kuyo imbiza esithombile, ukuthomba kwayo okungayikuphela! Thulula imbiza ukhuphe amaqhatha ngalinye ngalinye kungekho inkatho.
7 “‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
Ngakho igazi elachithwa lidolobho leli liphakathi kwalo: lalithululela edwaleni elize; kalilithululelanga phansi lapho umhlabathi owawungaligqibela khona.
8 Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
Ukuze ngivuse intukuthelo njalo ngiphindisele, ngabeka igazi lelo phezu kwedwala elize, ukuze lingagqitshelwa.
9 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
Ngakho nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi: Maye kulo idolobho lokuchithwa kwegazi! Lami futhi, ngizakwenza ibonda lenkuni eliphakemeyo.
10 Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
Ngakho faka inkuni uphembe umlilo. Ipheke kuhle inyama, uhlanganisa leziyoliso; uyekele amathambo atshe.
11 Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
Emva kwalokho beka imbiza engelalutho phezu kwamalahle ize itshise lethusi layo livuthe ukuze ukungcola kwayo kutshe kuphele lokuthomba kwayo kutshe kuphele.
12 Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
Isiphuthise imizamo yonke; uqweqwe lokuthomba kwayo kalususwanga, loba langomlilo.
13 “‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
Khathesi ukungcola kwakho yisigwebo. Ngoba ngizamile ukukuhlambulula kodwa ubungeke uhlanjululwe ekungcoleni kwakho, kawuyikuhlambuluka futhi ukukuthukuthelela kwami kuze kudede.
14 “‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Mina Thixo sengikhulumile. Isikhathi sokuba ngenze sesifikile. Kangiyikuzithiba; kangiyikuba lesihawu, kumbe ngiyekethise. Uzakwahlulelwa mayelana lokuziphatha kwakho kanye lezenzo zakho, kutsho uThixo Wobukhosi.’”
15 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ilizwi likaThixo lafika kimi lisithi:
16 “Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
“Ndodana yomuntu, sekuseduze ukuthi ngokugalela okukodwa nje ngisuse kuwe intokozo yamehlo akho. Kodwa ungalili kumbe ukhale loba wehlise inyembezi.
17 Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
Bubula uthule; ungalileli abafileyo. Bophela iqhiye yakho lamanyathela akho ezinyaweni zakho; ungambozi ingxenye yaphansi yobuso bakho loba udle ukudla komkhuba wabalilayo.”
18 Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
Ngakho ngakhuluma labantu ekuseni, umkami wafa kusihlwa. Ekuseni kwakusisa ngenza njengokulaywa kwami.
19 Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
Abantu basebengibuza besithi, “Kawuyikusitshela na ukuthi izinto lezi zilani lathi?”
20 Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
Ngakho mina ngathi kubo, “Ilizwi likaThixo lafika kimi lisithi:
21 faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
Tshono endlini ka-Israyeli uthi, ‘Nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi: Sekuseduze ukuthi ngingcolise indlu yami engcwele, inqaba eliziqhenya ngayo, intokozo yamehlo enu, into eliyithanda kakhulu. Amadodana lamadodakazi eliwatshiyileyo azabulawa ngenkemba.
22 Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
Njalo lizakwenza njengoba ngenzile. Kaliyikumboza ingxenye yaphansi yobuso benu loba lidle ukudla komkhuba wabalilayo.
23 Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
Lizafaka amaqhiye enu emakhanda enu lamanyathela enu ezinyaweni zenu. Kaliyikulila kumbe likhale kodwa lizacikizeka ngenxa yezono zenu njalo libubule phakathi kwenu.
24 Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
UHezekhiyeli uzakuba yisibonakaliso kini; lizakwenza njengoba enzile. Nxa lokhu kusenzakala, lizakwazi ukuthi mina nginguThixo Wobukhosi.’
25 “Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
Njalo wena, ndodana yomuntu, ngosuku engizasusa ngalo inqaba yabo, intokozo yabo lodumo, injabulo yamehlo abo, isifiso senhliziyo yabo, kanye lamadodana lamadodakazi abo futhi,
26 a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
ngalolosuku isiphepheli yiso esizalandisa izindaba.
27 A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”
Ngalesosikhathi umlomo wakho uzavuleka; uzakhuluma laye njalo kawuyikuthula futhi. Ngakho uzakuba yisibonakaliso kubo, njalo bazakwazi ukuthi nginguThixo.”