< Ezekiyel 17 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of Jehovah came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
Son of man, put forth a riddle, and speak a parable to the house of Israel,
3 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
and say, Thus says the lord Jehovah: A great eagle with great wings and long pinions, full of feathers, which had various colors, came to Lebanon, and took the top of the cedar.
4 ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
He cropped off the topmost of the young twigs of it, and carried it to a land of merchandise. He set it in a city of merchants.
5 “‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
He took also of the seed of the land, and planted it in a fruitful soil. He placed it beside many waters. He set it as a willow tree.
6 ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
And it grew, and became a spreading vine of low stature, whose branches turned toward him, and the roots of it were under him. So it became a vine, and brought forth branches, and shot forth sprigs.
7 “‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
There was also another great eagle with great wings and many feathers. And, behold, this vine bent its roots toward him, and shot forth its branches toward him, from the beds of its plantation, that he might water it.
8 An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
It was planted in a good soil by many waters that it might bring forth branches, and that it might bear fruit that it might be a goodly vine.
9 “Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
Say thou, Thus says the lord Jehovah: Shall it flourish? Shall he not pull up the roots of it, and cut off the fruit of it, that it may wither? It shall wither in all its fresh springing leaves, even without great power or many people to pluck it up by the roots of it.
10 Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
Yea, behold, being planted, shall it flourish? Shall it not utterly wither when the east wind touches it? It shall wither in the beds where it grew.
11 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Moreover the word of Jehovah came to me, saying,
12 “Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
Say now to the rebellious house, Know ye not what these things mean? Tell them, Behold, the king of Babylon came to Jerusalem, and took the king of it, and the rulers of it, and brought them to him to Babylon.
13 Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
And he took of the seed royal, and made a covenant with him. He also brought him under an oath, and took away the mighty of the land,
14 don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
that the kingdom might be base, that it might not lift itself up, but that by keeping his covenant it might stand.
15 Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
But he rebelled against him in sending his ambassadors into Egypt that they might give him horses and many people. Shall he prosper? Shall he escape who does such things? Shall he break the covenant, and yet escape?
16 “‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
As I live, says the lord Jehovah, surely in the place where the king dwells who made him king, whose oath he despised, and whose covenant he broke, even with him in the midst of Babylon he shall die.
17 Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
Nor shall Pharaoh with his mighty army and great company help him in the war when they cast up mounds and build forts to cut off many persons.
18 Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
For he has despised the oath by breaking the covenant. And, behold, he had given his hand, and yet has done all these things. He shall not escape.
19 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
Therefore thus says the lord Jehovah: As I live, surely my oath that he has despised, and my covenant that he has broken, I will even bring it upon his own head.
20 Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
And I will spread my net upon him, and he shall be taken in my snare. And I will bring him to Babylon, and will enter into judgment with him there for his trespass that he has trespassed against me.
21 Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
And all his fugitives in all his groups shall fall by the sword, and those who remain shall be scattered toward every wind. And ye shall know that I, Jehovah, have spoken it.
22 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
Thus says the lord Jehovah: I will also take of the lofty top of the cedar, and will set it. I will crop off a tender one from the topmost of its young twigs, and I will plant it upon a high and lofty mountain.
23 A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
I will plant it in the mountain of the height of Israel, and it shall bring forth boughs, and bear fruit, and be a goodly cedar. And all birds of every wing shall dwell under it; they shall dwell in the shade of the branches thereof.
24 Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”
And all the trees of the field shall know that I, Jehovah, have brought down the high tree, have exalted the low tree, have dried up the green tree, and have made the dry tree to flourish. I, Jehovah, have spoken and have done it.

< Ezekiyel 17 >