< Makoki 1 >

1 Yanzu birnin ya zama babu kowa a ciki, birnin da a dā yake cike da mutane! Yanzu birnin ya zama kamar gwauruwa, wadda a dā babba ce ita a cikin ƙasashe! Ita da take sarauniya a cikin larduna yanzu ta zama baiwa.
How the city sits solitary, that was full of people! She has become as a widow, who was great among the nations! She who was a princess among the provinces has become tributary!
2 Tana yin kuka mai zafi da dare, hawaye na gangara a kan kumatunta. A cikin masoyanta duka babu wanda ya yi mata ta’aziyya. Duk abokanta sun yashe ta; sun zama abokan gābanta.
She weeps bitterly in the night, and her tears are on her cheeks. Among all her loved ones she has none to comfort her. All her friends have dealt treacherously with her, they have become her enemies.
3 Bayan wahala da baƙin ciki, Yahuda ta tafi bauta. Ta zauna a cikin ƙasashe, ba tă samu wurin hutawa ba. Duk masu fafararta sun same ta sa’ad da take cikin matuƙar ɓacin rai.
Judah has gone into captivity because of affliction. And because of great servitude she dwells among the nations. She finds no rest. All her persecutors overtook her in the distress.
4 Hanyoyin zuwa Sihiyona suna makoki, gama ba wanda ya zo bikin da ta shirya. Ba kowa a hanyoyin shiganta. Firistocinta suna gurnani,’yan matana kuma suna wahala, kuma tana cikin shan wahala ƙwarai.
The ways of Zion mourn, because none come to the solemn assembly. All her gates are desolate. Her priests sigh. Her virgins are afflicted, and she herself is in bitterness.
5 Maƙiyanta sun zama shugabanninta; Abokan gābanta suna da kwanciyar rai. Ubangiji ya kawo mata ɓacin rai domin yawan zunubanta.’Ya’yanta sun tafi bauta, a ƙarƙashin maƙiyanta.
Her adversaries have become the head. Her enemies prosper. For Jehovah has afflicted her for the multitude of her transgressions. Her young sons have gone into captivity before the adversary.
6 Diyar Sihiyona ba ta da sauran daraja.’Ya’yan sarakunanta sun zama kamar bareyi waɗanda suka rasa wurin kiwo; cikin rashin ƙarfi suka guje wa masu fafararsu.
And from the daughter of Zion all her majesty is departed. Her rulers have become like harts that find no pasture. And they have gone without strength before the pursuer.
7 A cikin kwanakin da take shan wahala take kuma yawo Urushalima ta tuna da dukan dukiyar da take da ita a kwanakin dā can. Sa’ad da mutanenta suka faɗa cikin hannun abokan gābanta, ba wanda ya taimake ta. Maƙiyanta suka dube ta suka yi mata dariya don hallakar da ta auko mata.
Jerusalem remembers in the days of her affliction and of her miseries all her pleasant things that were from the days of old. When her people fell into the hand of the adversary, and none helped her, the adversaries saw her; they mocked at her desolations.
8 Urushalima ta yi zunubi ƙwarai saboda haka ta zama marar tsarki. Dukan masu martaba ta sun raina ta, gama sun ga tsiraicinta; ita ma da kanta tana nishi da ƙyar ta kuma juya baya.
Jerusalem has grievously sinned, therefore she has become as an unclean thing. All who honored her despise her, because they have seen her nakedness. Yea, she sighs, and turns backward.
9 Ƙazantarta ta manne wa rigunanta; ba tă kula da nan gaba ba, fāɗuwarta kuwa babban abu ne; babu wanda zai yi mata ta’aziyya. “Duba, ya Ubangiji, ka ga wahalata, gama maƙiyi ya yi nasara.”
Her filthiness was in her skirts. She did not think of her latter end. Therefore she has come down astonishingly. She has no comforter. Behold, O Jehovah, my affliction, for the enemy has magnified himself.
10 Maƙiya ya kwashe dukiyarta duka; ta ga mutanen da ba su san Allah ba sun shiga wuri mai tsarkinta waɗanda ka hana su shiga taron jama’arka.
The adversary has spread out his hand upon all her pleasant things. For she has seen that the nations have entered into her sanctuary, concerning whom thou commanded that they should not enter into thine assembly.
11 Dukan mutanenta suna nishi da ƙyar suna neman burodi; sun sayar da dukiyarsu don su samu abinci don kada su mutu da yunwa. “Ubangiji, ka duba ka gani, gama an yashe ni.”
All her people sigh. They seek bread. They have given their pleasant things for food to refresh the soul. See, O Jehovah, and, behold, for I have become abject.
12 “Ko wannan ba wani abu ba ne a wurinku, dukanku masu wucewa? Ku duba ku gani. Ko akwai wata wahala kamar irin wadda nake sha, wadda Ubangiji ya auko mini a cikin zafin fushinsa?
Is it nothing to you, all ye who pass by? Behold, and see if there is any sorrow like my sorrow, which is brought upon me. Therewith Jehovah has afflicted in the day of his fierce anger.
13 “Daga sama ya aiko da wuta, ya aiko ta cikin ƙasusuwana. Ya shimfiɗa raga a ƙafafuna ya juyo da ni. Ya bar ni ni kaɗai, sumamme dukan yini.
From on high he has sent fire into my bones, and it prevails against them. He has spread a net for my feet. He has turned me back. He has made me desolate and faint all the day.
14 “Ya ɗaura zunubaina a wuyana; aka naɗe su a hannuwansa. Aka rataye su a wuyana Ubangiji ya kwashe ƙarfina. Ya bashe ni ga waɗanda suka fi ni ƙarfi.
The yoke of my transgressions is bound by his hand. They are knit together. They have come up upon my neck. He has made my strength to fail. The Lord has delivered me into their hands, against whom I am not able to stand.
15 “Ubangiji ya ƙi duk mayaƙan da suke tare da ni; ya sa wata runduna ta tayar mini ta kuma tattake samarina. Ubangiji ya tattake budurwa Diyar Yahuda kamar’ya’yan inabi a wurin matsewa.
The Lord has trodden under foot all my mighty men in the midst of me. He has called a solemn assembly against me to crush my young men. The Lord has trodden the virgin daughter of Judah as in a winepress.
16 “Dalilin da ya sa nake kuka ke nan idanuna kuma suna ta zubar da hawaye. Babu wani a kusa da zai yi mini ta’aziyya, ba wanda zai sabunta ruhuna.’Ya’yana sun zama fakirai domin maƙiyina ya yi nasara.”
For these things I weep. My eye, my eye runs down with water, because the comforter who should refresh my soul is far from me. My sons are desolate, because the enemy has prevailed.
17 Sihiyona ta miƙa hannunta, amma ba wani da zai yi mata ta’aziyya. Ubangiji ya umarta cewa maƙwabtansa za su zama maƙiyansa; Urushalima ta zama abar ƙyama a cikinsu.
Zion spreads forth her hands. There is none to comfort her. Jehovah has commanded concerning Jacob, that those who are round about him should be his adversaries. Jerusalem is among them as an unclean thing.
18 “Ubangiji mai adalci ne, duk da haka na yi tawaye da umarninsa. Ku saurara, jama’a duka; ku dubi wahalar da nake sha. Samarina da’yan matana duka sun tafi bauta.
Jehovah is righteous, for I have rebelled against his commandment. Hear, I pray you, all ye peoples, and behold my sorrow. My virgins and my young men have gone into captivity.
19 “Na kira abokaina amma sun yashe ni. Firistocina da dattawana sun hallaka a cikin birnin yayinda suke neman abinci don kada su mutu da yunwa.
I called for my loved ones, but they deceived me. My priests and my elders gave up the spirit in the city, while they sought food for themselves to refresh their souls.
20 “Duba, Ubangiji, ka ga ƙuncin da nake ciki! Ina shan azaba a raina, ba ni da kwanciyar rai a cikin zuciyata, domin na yi tawaye sosai. A waje takobi na kisa; a ciki kuma akwai mutuwa.
Behold, O Jehovah, for I am in distress. My heart is troubled. My heart is turned within me. For I have grievously rebelled. Abroad the sword bereaves; at home there is as death.
21 “Mutane suna ji ina nishi da ƙyar, amma ba wanda zai yi mini ta’aziyya. Dukan maƙiyana sun ji wahalar da nake ciki; suna farin ciki da abin da ka yi. Ka kawo ranan nan da ka sanar domin su ma su zama kamar ni.
They have heard that I sigh. There is none to comfort me. All my enemies have heard of my trouble. They are glad that thou have done it. Thou will bring the day that thou have proclaimed, and they shall be like me.
22 “Bari ka ga muguntarsu duka; ka yi musu yadda ka yi mini domin dukan zunubansu. Nishina da yawa kuma zuciyata ta gaji.”
Let all their wickedness come before thee, and do to them, as thou have done to me for all my transgressions. For my sighs are many, and my heart is faint.

< Makoki 1 >