< Ezekiyel 15 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
E veiu a mim a palavra do Senhor, dizendo:
2 “Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
Filho do homem, que mais é o pau da videira do que todo outro pau? ou o sarmento entre os paus do bosque?
3 An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
Toma-se porventura d'elle madeira para fazer alguma obra? ou toma-se d'elle alguma estaca, para que se lhe pendure algum traste?
4 Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
Eis que o entregam ao fogo, para que seja consumido; ambas as suas extremidades consome o fogo, e o meio d'elle fica queimado: serviria porventura para alguma obra?
5 In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
Eis que, estando inteiro, não se fazia d'elle obra, quanto menos sendo consumido do fogo? e, sendo queimado, se faria ainda obra d'elle?
6 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
Portanto, assim diz o Senhor Jehovah: Como é o pau da videira entre os paus do bosque, o que entrego ao fogo para que seja consumido, assim entregarei os habitantes de Jerusalem.
7 Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Porque porei a minha face contra elles; saindo elles de um fogo, outro fogo os consumirá; e sabereis que eu sou o Senhor, quando tiver posto a minha face contra elles.
8 Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
E tornarei a terra em assolação, porquanto grandemente prevaricaram, diz o Senhor Jehovah.

< Ezekiyel 15 >