< Ezekiyel 14 >

1 Waɗansu dattawan Isra’ila suka zo wurina suka zauna a ƙasa a gabana.
E vieram a mim alguns homens dos anciãos de Israel, e se assentaram diante de mim.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Então veiu a mim a palavra do Senhor, dizendo:
3 “Ɗan mutum, waɗannan mutane sun kafa gumaka a cikin zukatansu suka sa mugayen abubuwan sa tuntuɓe a gabansu. Zan bar su, su taɓa nemi ni?
Filho do homem, estes homens levantaram os seus idolos sobre os seus corações, e o tropeço da sua maldade pozeram diante da sua face; porventura pois devéras me perguntam?
4 Saboda haka ka yi musu magana ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da wani mutumin Isra’ila ya kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuma sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina game da babban bautar gumakarsa.
Portanto falla com elles, e dize-lhes: Assim diz o Senhor Jehovah: Qualquer homem da casa de Israel, que levantar os seus idolos sobre o seu coração, e o tropeço da sua maldade pozer diante da sua face, e vier ao propheta, eu, o Senhor, vindo elle, lhe responderei conforme a multidão dos seus idolos;
5 Zan yi haka don in sāke ƙame zukatan mutanen Isra’ila, waɗanda duk suka yashe ni don gumakansu.’
Para apanhar a casa de Israel no seu coração, porquanto todos se apartaram de mim para seguirem os seus idolos.
6 “Saboda haka ka faɗa wa gidan Isra’ila cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tuba! Ku juyo daga gumakanku ku kuma furta dukan ayyukanku masu banƙyama!
Portanto dize á casa de Israel: Assim diz o Senhor Jehovah: Convertei-vos, e deixae-vos converter dos vossos idolos; e desviae os vossos rostos de todas as vossas abominações.
7 “‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
Porque qualquer homem da casa de Israel, e dos estrangeiros que peregrinam em Israel, que se alienar de mim, e levantar os seus idolos sobre o seu coração, e pozer o tropeço da sua maldade diante do seu rosto, e vier ao propheta, para me consultar por meio d'elle, eu, o Senhor, lhe responderei por mim mesmo.
8 Zan yi gāba da mutumin in kuma sa ya zama misali da kuma abin karin magana. Zan ware shi daga mutanena. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
E porei o meu rosto contra o tal homem, e o assolarei para que sirva de signal e de dictado, e arrancal-o-hei do meio do meu povo: e sabereis que eu sou o Senhor.
9 “‘In kuma aka ruɗi annabin har ya yi annabci, Ni Ubangiji na rinjayi wannan annabi, zan kuma miƙa hannuna gāba da shi in hallaka shi daga cikin mutanena Isra’ila.
E quando o propheta se deixar persuadir, e fallar alguma coisa, eu, o Senhor, persuadi esse propheta; e estenderei a minha mão contra elle, e destruil-o-hei do meio do meu povo Israel,
10 Za su ɗauki hakkin laifinsu annabin zai zama mai laifi daidai da wanda ya zo neman shawararsa.
E levarão a sua maldade: como fôr a maldade do que pergunta, assim será a maldade do propheta;
11 Sa’an nan mutanen Isra’ila ba za su ƙara kauce daga gare ni ba, ba kuwa za su ƙara ƙazantar da kansu da dukan zunubansu ba. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Para que a casa de Israel não se desvie mais d'após mim, nem se contamine mais com todas as suas transgressões: então elles me serão por povo, e eu lhes serei por Deus, diz o Senhor Jehovah.
12 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Veiu ainda a mim a palavra do Senhor, dizendo:
13 “Ɗan mutum, in wata ƙasa ta yi mini zunubi ta wurin rashin aminci na kuma miƙa hannuna gāba da ita don in toshe hanyar samun abincinta na kuma aika da yunwa a kanta na kashe mutanenta da dabbobinta,
Filho do homem, quando uma terra peccar contra mim, gravemente rebellando, então estenderei a minha mão contra ella, e lhe quebrarei o sustento do pão, e enviarei contra ella fome, e arrancarei d'ella homens e animaes:
14 ko da waɗannan mutum uku Nuhu, Daniyel da kuma Ayuba suna a cikinta, za su iya ceton kansu ne kawai ta wurin adalcinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Ainda que estivessem no meio d'ella estes tres homens, Noé, Daniel e Job, elles pela sua justiça livrariam sómente a sua alma, diz o Senhor Jehovah.
15 “Ko kuwa in na aika da namun jeji su ratsa cikin wannan ƙasa suka kuma bar ta babu yaro, ta kuma zama kufai har babu wanda zai ratsa cikinta saboda namun jeji,
Se eu fizer passar pela terra as más bestas, e ellas a despojarem de filhos, que ella seja assolada, e ninguem possa passar por ella por causa das bestas;
16 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da ma waɗannan mutum uku suna a cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto, amma ƙasar za tă zama kufai.
E estes tres homens estivessem no meio d'ella, vivo eu, diz o Senhor Jehovah, que nem a filhos nem a filhas livrariam; elles só ficariam livres, e a terra seria assolada.
17 “Ko kuma in na kawo takobi a kan wannan ƙasa na kuma ce, ‘Bari takobin ya ratsa cikin dukan ƙasar,’ na kuma kashe mutanenta da dabbobinsu,
Ou, se eu trouxer a espada sobre a tal terra, e disser: Espada, passa pela terra: e eu arrancar d'ella homens e bestas:
18 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da waɗannan mutum uku suna cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto.
Ainda que aquelles tres homens estivessem n'ella, vivo eu, diz o Senhor Jehovah, que nem filhos nem filhas livrariam, senão elles só ficariam livres.
19 “Ko kuma in na aika da annoba a cikin wannan ƙasa na kuma yi fushi a kanta ta wurin kisa, ina kisan mutanenta da dabbobinsu,
Ou, se eu enviar a peste sobre a tal terra, e derramar o meu furor sobre ella com sangue, para arrancar d'ella homens e bestas:
20 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da Nuhu, Daniyel da Ayuba suna a cikinta, ba za su iya ceton ɗansu ko’yarsu ba. Za su iya ceton kansu ne kaɗai ta wurin adalcinsu.
Ainda que Noé, Daniel e Job estivessem no meio d'ella, vivo eu, diz o Senhor Jehovah, que nem um filho nem uma filha livrariam a sua alma, mas só elles livrarão as suas proprias almas pela sua justiça.
21 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa balle fa sa’ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi takobi da yunwa da namun jeji da annoba don su kashe mutanenta da dabbobinsu!
Porque assim diz o Senhor Jehovah: Quanto mais, se eu enviar os meus quatro maus juizos, a espada, e a fome, e as más bestas, e a peste, contra Jerusalem, para arrancar d'ella homens e bestas?
22 Duk da haka za a sami mutanen da za su ragu’ya’ya maza da matan da za a fitar daga cikinta. Za su zo wurinka, kuma sa’ad da ka gan halinsu da ayyukansu, za ka ta’azantu game da bala’in da na kawo a kan Urushalima kowane bala’in da na kawo a kanta.
Porém eis que alguns dos que escaparem ficarão de resto n'ella, que serão tirados para fóra, assim filhos como filhas; eis que elles sairão a vós, e vereis o seu caminho e os seus feitos; e ficareis consolados do mal que eu trouxe sobre Jerusalem, e de tudo o que trouxe sobre ella.
23 Za ka ta’azantu sa’ad da ka ga halinsu da kuma ayyukansu, gama za ka san cewa ban aikata wani abu a cikinta ba dalili ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
E vos consolarão, quando virdes o seu caminho e os seus feitos; e sabereis que não fiz sem razão tudo quanto fiz n'ella, diz o Senhor Jehovah.

< Ezekiyel 14 >