< Ezekiyel 14 >
1 Waɗansu dattawan Isra’ila suka zo wurina suka zauna a ƙasa a gabana.
Potem so prišli k meni nekateri izmed Izraelovih starešin in se usedli pred menoj.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
In k meni je prišla Gospodova beseda, rekoč:
3 “Ɗan mutum, waɗannan mutane sun kafa gumaka a cikin zukatansu suka sa mugayen abubuwan sa tuntuɓe a gabansu. Zan bar su, su taɓa nemi ni?
»Človeški sin, ti možje so si v srcih postavljali malike in so si pred svoj obraz postavljali kamen spotike svoje krivičnosti; ali naj bi me oni potem sploh spraševali?«
4 Saboda haka ka yi musu magana ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da wani mutumin Isra’ila ya kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuma sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina game da babban bautar gumakarsa.
Zato jim govori in jim povej: »Tako govori Gospod Bog: ›Vsak mož iz Izraelove hiše, ki si v svojem srcu postavlja malike in pred svoj obraz polaga kamen spotike svoje krivičnosti in prihaja k preroku; jaz, Gospod, bom odgovoril tistemu, ki prihaja, glede na množico njegovih malikov,
5 Zan yi haka don in sāke ƙame zukatan mutanen Isra’ila, waɗanda duk suka yashe ni don gumakansu.’
da bi Izraelovo hišo lahko ujel v njihovem lastnem srcu, ker so se zaradi svojih malikov vsi odtujili od mene.‹
6 “Saboda haka ka faɗa wa gidan Isra’ila cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tuba! Ku juyo daga gumakanku ku kuma furta dukan ayyukanku masu banƙyama!
Zato reci Izraelovi hiši: ›Tako govori Gospod Bog: ›Pokesajte se in odvrnite se od svojih malikov; odvrnite svoje obraze od vseh svojih ogabnosti.‹
7 “‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
Kajti vsakomur izmed Izraelove hiše, ali izmed tujca, ki začasno biva v Izraelu, ki se ločuje od mene in si v svojem srcu postavlja svoje malike in polaga kamen spotike svoje krivičnosti pred svoj obraz in prihaja k preroku, da bi od njega povprašal glede mene, mu bom jaz, Gospod, sam odgovoril.
8 Zan yi gāba da mutumin in kuma sa ya zama misali da kuma abin karin magana. Zan ware shi daga mutanena. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Svoj obraz bom naravnal zoper tega moža in naredil ga bom za znamenje in pregovor in odrezal ga bom iz srede svojega ljudstva; in spoznali boste, da jaz sem Gospod.
9 “‘In kuma aka ruɗi annabin har ya yi annabci, Ni Ubangiji na rinjayi wannan annabi, zan kuma miƙa hannuna gāba da shi in hallaka shi daga cikin mutanena Isra’ila.
Če pa je prerok zaveden, ko je govoril besedo, sem jaz, Gospod, zavedel tega preroka in jaz bom iztegnil svojo roko nanj in ga uničim iz srede svojega ljudstva Izraela.
10 Za su ɗauki hakkin laifinsu annabin zai zama mai laifi daidai da wanda ya zo neman shawararsa.
Nosila bosta kazen svoje krivičnosti. Kazen preroka bo celo kakor kazen tistega, ki poizveduje k njemu;
11 Sa’an nan mutanen Isra’ila ba za su ƙara kauce daga gare ni ba, ba kuwa za su ƙara ƙazantar da kansu da dukan zunubansu ba. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
da Izraelova hiša ne bo več zašla od mene niti ne bo več oskrunjena z vsemi svojimi prestopki; temveč da bodo lahko moje ljudstvo in bom jaz lahko njihov Bog, govori Gospod Bog.‹«
12 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Gospodova beseda je prišla ponovno k meni, rekoč:
13 “Ɗan mutum, in wata ƙasa ta yi mini zunubi ta wurin rashin aminci na kuma miƙa hannuna gāba da ita don in toshe hanyar samun abincinta na kuma aika da yunwa a kanta na kashe mutanenta da dabbobinta,
»Človeški sin, kadar dežela greši zoper mene z mučnimi prekršitvami, takrat bom nadnjo iztegnil svojo roko in zlomil bom njeno oporo kruha in nadnjo bom poslal lakoto in iz nje bom iztrebil človeka in žival.
14 ko da waɗannan mutum uku Nuhu, Daniyel da kuma Ayuba suna a cikinta, za su iya ceton kansu ne kawai ta wurin adalcinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Čeprav bi bili v njej ti trije možje: Noe, Daniel in Job, bi s svojo pravičnostjo rešili zgolj svoje lastne duše, ‹ govori Gospod Bog.
15 “Ko kuwa in na aika da namun jeji su ratsa cikin wannan ƙasa suka kuma bar ta babu yaro, ta kuma zama kufai har babu wanda zai ratsa cikinta saboda namun jeji,
›Če povzročim ogabnim živalim, da gredo skozi deželo, jo oplenijo tako, da je ta zapuščena, da zaradi živali noben človek ne bo mogel iti skoznjo;
16 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da ma waɗannan mutum uku suna a cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto, amma ƙasar za tă zama kufai.
čeprav bi bili ti trije možje v njej, kakor jaz živim, ‹ govori Gospod Bog, ›ne bodo osvobodili niti sinov niti hčera; samo oni sami bodo osvobojeni, toda dežela bo zapuščena.
17 “Ko kuma in na kawo takobi a kan wannan ƙasa na kuma ce, ‘Bari takobin ya ratsa cikin dukan ƙasar,’ na kuma kashe mutanenta da dabbobinsu,
Ali če privedem meč nad to deželo in rečem: ›Meč, pojdi skozi to deželo; ‹ tako, da iz nje iztrebim ljudi in živali;
18 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da waɗannan mutum uku suna cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto.
čeprav bi bili ti trije možje v njej, kakor jaz živim, ‹ govori Gospod Bog, ›ne bi osvobodili niti sinov niti hčera; samo oni sami bi bili osvobojeni.
19 “Ko kuma in na aika da annoba a cikin wannan ƙasa na kuma yi fushi a kanta ta wurin kisa, ina kisan mutanenta da dabbobinsu,
Ali če pošljem v to deželo kužno bolezen in če nanjo v krvi izlijem svojo razjarjenost, da iztrebim iz nje človeka in žival;
20 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da Nuhu, Daniyel da Ayuba suna a cikinta, ba za su iya ceton ɗansu ko’yarsu ba. Za su iya ceton kansu ne kaɗai ta wurin adalcinsu.
čeprav bi bili v njej Noe, Daniel in Job, kakor jaz živim, ‹ govori Gospod Bog, ›ne bi osvobodili niti sinov niti hčera, temveč bodo po svoji pravičnosti osvobodili zgolj svoje lastne duše.‹
21 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa balle fa sa’ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi takobi da yunwa da namun jeji da annoba don su kashe mutanenta da dabbobinsu!
Kajti tako govori Gospod Bog: ›Koliko bolj, ko pošljem svoje štiri boleče sodbe nad Jeruzalem: meč, lakoto in ogabno zver in kužno bolezen, da iztrebim iz nje ljudi in živali?
22 Duk da haka za a sami mutanen da za su ragu’ya’ya maza da matan da za a fitar daga cikinta. Za su zo wurinka, kuma sa’ad da ka gan halinsu da ayyukansu, za ka ta’azantu game da bala’in da na kawo a kan Urushalima kowane bala’in da na kawo a kanta.
In vendar, glejte, bo tam ostal ostanek, ki bo izpeljan, tako sinov kakor hčera. Glejte, prišli bodo k vam in videli boste njihovo pot in njihova dejanja in potolaženi boste glede zla, ki sem ga privedel nad Jeruzalem, celó glede vsega, kar sem privedel nadenj.
23 Za ka ta’azantu sa’ad da ka ga halinsu da kuma ayyukansu, gama za ka san cewa ban aikata wani abu a cikinta ba dalili ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
In potolažili vas bodo, ko boste videli njihove poti in njihova dejanja, in spoznali boste, da nisem brez vzroka storil vsega, kar sem storil v njem, ‹ govori Gospod Bog.‹«