< Makoki 1 >

1 Yanzu birnin ya zama babu kowa a ciki, birnin da a dā yake cike da mutane! Yanzu birnin ya zama kamar gwauruwa, wadda a dā babba ce ita a cikin ƙasashe! Ita da take sarauniya a cikin larduna yanzu ta zama baiwa.
Kako mesto sedi osamljeno, ki je bilo polno ljudstva! Kako je ona postala kakor vdova! Ona, ki je bila velika med narodi in princesa med provincami, kako je postala podvržena davku!
2 Tana yin kuka mai zafi da dare, hawaye na gangara a kan kumatunta. A cikin masoyanta duka babu wanda ya yi mata ta’aziyya. Duk abokanta sun yashe ta; sun zama abokan gābanta.
Bridko joka ponoči in njene solze so na njenih licih. Med vsemi svojimi ljubimci nima nikogar, da jo potolaži. Vsi njeni prijatelji so zahrbtno postopali z njo, postali so njeni sovražniki.
3 Bayan wahala da baƙin ciki, Yahuda ta tafi bauta. Ta zauna a cikin ƙasashe, ba tă samu wurin hutawa ba. Duk masu fafararta sun same ta sa’ad da take cikin matuƙar ɓacin rai.
Juda je odšel v ujetništvo zaradi stiske in zaradi velikega hlapčevstva. Prebiva med pogani, ne najde nobenega počitka. Vsi njegovi preganjalci so ga dohiteli med ožinami.
4 Hanyoyin zuwa Sihiyona suna makoki, gama ba wanda ya zo bikin da ta shirya. Ba kowa a hanyoyin shiganta. Firistocinta suna gurnani,’yan matana kuma suna wahala, kuma tana cikin shan wahala ƙwarai.
Poti [na] Sion žalujejo, ker ni nihče prišel k slovesnim praznikom. Vsa njena velika vrata so zapuščena. Njeni duhovniki vzdihujejo, njene device so užaloščene in sama je v grenkobi.
5 Maƙiyanta sun zama shugabanninta; Abokan gābanta suna da kwanciyar rai. Ubangiji ya kawo mata ɓacin rai domin yawan zunubanta.’Ya’yanta sun tafi bauta, a ƙarƙashin maƙiyanta.
Njeni nasprotniki so vodilni, njeni sovražniki uspevajo; kajti Gospod jo je prizadel zaradi množice njenih prestopkov. Njeni otroci so odšli v ujetništvo pred sovražnikom.
6 Diyar Sihiyona ba ta da sauran daraja.’Ya’yan sarakunanta sun zama kamar bareyi waɗanda suka rasa wurin kiwo; cikin rashin ƙarfi suka guje wa masu fafararsu.
Od sionske hčere je odšla vsa njena lepota. Njeni princi so postali podobni jelenom, ki ne najdejo pašnika in odšli so brez moči pred zasledovalcem.
7 A cikin kwanakin da take shan wahala take kuma yawo Urushalima ta tuna da dukan dukiyar da take da ita a kwanakin dā can. Sa’ad da mutanenta suka faɗa cikin hannun abokan gābanta, ba wanda ya taimake ta. Maƙiyanta suka dube ta suka yi mata dariya don hallakar da ta auko mata.
V dneh svoje stiske in svojih bed se je [prestolnica] Jeruzalem spomnila vseh svojih prijetnih stvari, ki jih je imela v dneh davnine, ko je njeno ljudstvo padlo v roko sovražnika in ji nihče ni pomagal. Nasprotniki so jo videli in jo zasmehovali pri njenih šabatih.
8 Urushalima ta yi zunubi ƙwarai saboda haka ta zama marar tsarki. Dukan masu martaba ta sun raina ta, gama sun ga tsiraicinta; ita ma da kanta tana nishi da ƙyar ta kuma juya baya.
[Prestolnica] Jeruzalem je bridko grešila, zato je odstranjena. Vsi, ki so jo častili, jo prezirajo, ker so videli njeno nagoto. Da, ona vzdihuje in se obrača nazaj.
9 Ƙazantarta ta manne wa rigunanta; ba tă kula da nan gaba ba, fāɗuwarta kuwa babban abu ne; babu wanda zai yi mata ta’aziyya. “Duba, ya Ubangiji, ka ga wahalata, gama maƙiyi ya yi nasara.”
Njena umazanost je v krajcih njenih oblačil; ne spominja se svojega zadnjega konca, zato se je čudovito spustila. Nobenega tolažnika ni imela. Oh Gospod, glej mojo stisko, kajti sovražnik se je poveličal.
10 Maƙiya ya kwashe dukiyarta duka; ta ga mutanen da ba su san Allah ba sun shiga wuri mai tsarkinta waɗanda ka hana su shiga taron jama’arka.
Nasprotnik je svojo roko razprostrl nad vse njene prijetne stvari, kajti videla je, da so pogani vstopili v njeno svetišče, katerim si zapovedal, da naj ne vstopijo v tvojo skupnost.
11 Dukan mutanenta suna nishi da ƙyar suna neman burodi; sun sayar da dukiyarsu don su samu abinci don kada su mutu da yunwa. “Ubangiji, ka duba ka gani, gama an yashe ni.”
Vse njeno ljudstvo vzdihuje, iščejo kruh; svoje prijetne stvari so dali za hrano, da podprejo dušo. Glej, oh Gospod in preudari, kajti postala sem ničvredna.
12 “Ko wannan ba wani abu ba ne a wurinku, dukanku masu wucewa? Ku duba ku gani. Ko akwai wata wahala kamar irin wadda nake sha, wadda Ubangiji ya auko mini a cikin zafin fushinsa?
Ali vam ni to nič, vsi vi, ki greste mimo? Glejte in vidite, če je tam kakršnakoli bridkost podobna moji bridkosti, ki mi je storjena, s katero me je Gospod prizadel na dan svoje krute jeze.
13 “Daga sama ya aiko da wuta, ya aiko ta cikin ƙasusuwana. Ya shimfiɗa raga a ƙafafuna ya juyo da ni. Ya bar ni ni kaɗai, sumamme dukan yini.
Od zgoraj je poslal ogenj v moje kosti in ta je prevladal zoper njih. Razprostrl je mrežo za moja stopala, obrnil me je nazaj. Naredil me je zapuščeno in ves dan slabim.
14 “Ya ɗaura zunubaina a wuyana; aka naɗe su a hannuwansa. Aka rataye su a wuyana Ubangiji ya kwashe ƙarfina. Ya bashe ni ga waɗanda suka fi ni ƙarfi.
Jarem mojih prestopkov je zvezan z njegovo roko. Oviti so in prišli so gor nad moj vrat. Moji moči je storil, da odpove, Gospod me je izročil v njihove roke, pred katerimi se nisem zmožen dvigniti.
15 “Ubangiji ya ƙi duk mayaƙan da suke tare da ni; ya sa wata runduna ta tayar mini ta kuma tattake samarina. Ubangiji ya tattake budurwa Diyar Yahuda kamar’ya’yan inabi a wurin matsewa.
Gospod je pod stopalom pomendral vse moje mogočne može v moji sredi. Zoper mene je sklical zbor, da zdrobi moje mladeniče. Gospod je pomendral devico, Judovo hčer, kakor v vinski stiskalnici.
16 “Dalilin da ya sa nake kuka ke nan idanuna kuma suna ta zubar da hawaye. Babu wani a kusa da zai yi mini ta’aziyya, ba wanda zai sabunta ruhuna.’Ya’yana sun zama fakirai domin maƙiyina ya yi nasara.”
Zaradi teh stvari jokam. Moje oko, moje oko teče dol z vodo, ker je tolažnik, ki naj bi razbremenil mojo dušo, daleč od mene. Moji otroci so zapuščeni, ker je sovražnik prevladal.
17 Sihiyona ta miƙa hannunta, amma ba wani da zai yi mata ta’aziyya. Ubangiji ya umarta cewa maƙwabtansa za su zama maƙiyansa; Urushalima ta zama abar ƙyama a cikinsu.
Sion razširja svoje roke in tam ni nikogar, da jo potolaži. Gospod je zapovedal glede Jakoba, da naj bi bili njegovi nasprotniki naokoli njega. [Prestolnica] Jeruzalem je med njimi kakor ženska, ki ima menstruacijo.
18 “Ubangiji mai adalci ne, duk da haka na yi tawaye da umarninsa. Ku saurara, jama’a duka; ku dubi wahalar da nake sha. Samarina da’yan matana duka sun tafi bauta.
Gospod je pravičen, kajti uprla sem se zoper njegovo zapoved. Poslušajte, prosim vas, vsa ljudstva in glejte mojo bridkost. Moje device in moji mladeniči so odšli v ujetništvo.
19 “Na kira abokaina amma sun yashe ni. Firistocina da dattawana sun hallaka a cikin birnin yayinda suke neman abinci don kada su mutu da yunwa.
Poklicala sem svoje ljubimce, toda oni so me zavedli. Moji duhovniki in moje starešine so v mestu izročili duha, medtem ko so iskali svojo hrano, da podprejo svoje duše.
20 “Duba, Ubangiji, ka ga ƙuncin da nake ciki! Ina shan azaba a raina, ba ni da kwanciyar rai a cikin zuciyata, domin na yi tawaye sosai. A waje takobi na kisa; a ciki kuma akwai mutuwa.
Glej, oh Gospod, kajti v tegobi sem. Moja notranjost je nemirna; moje srce je obrnjeno znotraj mene; kajti neposlušno sem se uprla. Zunaj ropa meč, doma je kakor smrt.
21 “Mutane suna ji ina nishi da ƙyar, amma ba wanda zai yi mini ta’aziyya. Dukan maƙiyana sun ji wahalar da nake ciki; suna farin ciki da abin da ka yi. Ka kawo ranan nan da ka sanar domin su ma su zama kamar ni.
Slišali so, da sem zavzdihnila. Tam ni nikogar, da me potolaži. Vsi moji sovražniki so slišali o moji stiski; veseli so, da si to storil. Privedel boš dan, ki si ga poklical in oni bodo podobni meni.
22 “Bari ka ga muguntarsu duka; ka yi musu yadda ka yi mini domin dukan zunubansu. Nishina da yawa kuma zuciyata ta gaji.”
Naj vsa njihova zlobnost pride predte, in stori jim, kakor si storil meni, zaradi vseh mojih prestopkov, kajti mojih vzdihov je mnogo in moje srce je oslabelo.

< Makoki 1 >