< Fitowa 12 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
BAWIPA ni Izip ram vah Mosi hoi Aron koe a dei pouh e teh;
2 “Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
Hete thapa heh nangmouh hanelah a kum tangkuem dawk apasuekpoung e thapa lah ao han.
3 Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
Nangmouh roi ni Isarel rangpuinaw koe lawk na thui roi hane teh; Hete thapa hnin hra touh hnin vah nangmanaw pueng ni mae imthungkhu tangkuem dawk im touh ni tuca buet touh rip na sin awh han.
4 In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
Imthung kathoeng teh tuca buet touh hoi kâki hoehpawiteh imri kahnai e koe a bawng vaiteh tami nâyittouh maw tie a parei hnukkhu, boung cakhuem hane tuca hah a sin han.
5 Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
Tuca thoseh, hmaeca thoseh, nangmouh ni na sin e saring teh kacueme hoi âvâ ka cawt hoeh rae a tan han.
6 Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
Hote tucanaw hah hote thapa hnin hra hlaipali totouh ring vaiteh, tangmin vah Isarel miphun, kamkhuengnaw ni a thei awh han.
7 Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
Tuca moi kacate im takhang tâphai hoi tangkhang dawk tu thi na hluk han.
8 A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
A moi teh hmai pahai hnukkhu, hote tangmin dawk tonphuenhoehe, kakhat e anhna hoi na ca awh han.
9 Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
Moi ka heng lah thoseh, thawng lahoi hai thoseh na cat awh mahoeh. A lû, a khok, a kosanaw hoi cungtalah hmai pahai hnukkhu na ca awh han.
10 Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
Hote moi hah khodai totouh na tat mahoeh. Youn touh hai na cawi sak pawiteh, hmai na sawi han.
11 Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
Bangtelamaw na ca awh han tetpawiteh, taisawm kâyeng hoi, khokkhawm hoi, sonron patuep lahoi karanglah na ca awh han. Hetteh, BAWIPA e ceitakhai pawi doeh.
12 “A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
Bangkongtetpawiteh, hote karum dawk Izip ram pueng dawk ka cei vaiteh Izipnaw e camin hoi saringnaw e ca caminnaw pueng ka thei han. Izipnaw e cathutnaw hah lawk ka ceng han. Kai teh BAWIPA doeh.
13 Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
Tuca e a thi teh nangmouh na onae im dawk nangmae mitnoutnae lah ao han. Hote a thi ka hmu navah, Kai ni nangmouh teh na ceitakhai awh han. Hottelah, Izip ram ka rek nah nangmouh karaphoekung lacik teh nangmouh koe phat mahoeh.
14 “Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
Hete hnin teh nangmouh hanlah pahnim thai hoeh e hnin lah ao vaiteh na ca catoun totouh, hete hnin dawk Cathut koe pawi a to awh han. Kâlawk lah ao dawkvah hote pawiteh pou na to awh han.
15 Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
Hnin sari touh thung tonphuenhoehe na ca awh han. Apasuek hnin nah ton hah imnaw dawk hoi na takhoe awh han. Apasuek hnin koehoi hnin sari totouh ton phuen e vaiyei ka cat e tami teh Isarel miphun dawk hoi takhoe lah ao han.
16 A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
Apasuek hnin thoseh, asari hnin nah thoseh kathoung kamkhuengnae na sak awh han. Hote hnin dawkvah, taminaw ni canei hoi kâkuen e thaw hloilah alouke thaw tawk awh mahoeh.
17 “Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
Hote tonphuenhoehe pawito ngainae teh, hote hnin dawk na taminaw Izip ram hoi ka tâco sak. Hatdawkvah, kâlawk ao e patetlah na ca catoun totouh hote hnin hah na ya awh han.
18 A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
Thapa yung pasuek, hnin hra hlaipali hnin tangmin hoi kamtawng teh hnin 20 tangmin totouh, nangmouh ni tonphuenhoehe na ca awh han.
19 Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
Hnin sari touh thung imnaw dawk ton na tat awh mahoeh. Ton phuen e vaiyei kacate ramlouk tami thoseh, khoca thoseh Isarelnaw koehoi takhoe lah ao han.
20 Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
Nangmouh na onae hmuen pueng koe ton phuen e vaiyei na cat awh mahoeh. Tonphuenhoehe vaiyei dueng na ca han atipouh.
21 Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
Hot navah, Mosi ni Isarel tami kacuenaw hah a kaw teh, na imthung tangkuem ni tuca hah ceitakhai pawi hanlah thet awh.
22 Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
Dingsala dawn lat awh nateh kawlung dawk ta e a thi dawk ranup nateh takhang dawk hluk awh. Hathnukkhu hoi amom totouh apihai ma im takhang alawilah na tâcawt a mahoeh.
23 Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
Bangkongtetpawiteh, BAWIPA teh Izipnaw thei hanlah a kâhlai han. Im takhang dawk e thi a hmu toteh BAWIPA ni takhang a ceitakhai han. Karaphoekung teh nangmouh reknae poe hanlah imthung kâen sak mahoeh.
24 “Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
Nangmouh hoi na canaw koe lawkkamnae ao dawkvah hote hno heh pou na tarawi awh han.
25 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
BAWIPA ni poe hanlah kam e ram dawk na pha awh toteh, hete phunglam heh na sak awh han.
26 Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
Nangmae ca catounnaw ni hete phung heh bang ngainae maw na sak telah na pacei pawiteh,
27 Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
BAWIPA ni Izipnaw a thei navah maimae imthungnaw a hlout sak. Izip ram kho ka sak e Isarelnaw e imnaw a ceitakhai e, BAWIPA e ceitakhai pawi lah ao telah bout na dei pouh han telah Mosi ni a dei hnukkhu, ahnimouh ni a lûsaling awh teh a bawk awh.
28 Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
BAWIPA ni Mosi hoi Aron koe lawk a thui e patetlah Isarelnaw ni a sak awh.
29 Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
Karumsaning vah, BAWIPA ni bawitungkhung dawk ka tahung e Faro e camin koehoi kamtawng teh thongkabawtnaw e camin totouh, Izipnaw e camin pueng thoseh, saringnaw e camin pueng thoseh koung a thei.
30 Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
Hote tangmin vah, Faro siangpahrang hoi a sannaw, Izipnaw ni a thaw awh teh, im tangkuem tami a due dawkvah, Izip ram pueng dawk khuikanae puenghoi a pha.
31 A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
Hote tangmin vah, Mosi hoi Aron a kaw teh, nangmouh roi hoi Isarelnaw thaw awh nateh ka taminaw koehoi tâcawt awh. Na hei e patetlah cet awh nateh Jehovah hah bawk awh leih.
32 Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
Nangmouh ni na hei e patetlah tu, maitonaw hrawi awh nateh cet awh. Kai haiyah yawhawinae na poe awh, telah atipouh.
33 Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
Izipnaw ni maimouh pueng hai tami kadout lah doeh koung o awh toe telah ati awh teh, Isarelnaw Izip ram dawk hoi karanglah tâco sak hanlah a dei pouh awh.
34 Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
Hote taminaw ni ton phuen hoeh rae tavai a la awh teh, tavai kanawknae kawlungnaw a la awh teh, hni hoi a tangoung awh teh a phu awh.
35 Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
Mosi ni a dei e patetlah Isarelnaw ni Izipnaw koe suingun, khohnanaw hah a hei awh.
36 Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
A hei awh e patetlah poe ngainae lungthin BAWIPA ni Izipnaw a tawn sak teh, Izipnaw e hnopainaw a lawp awh.
37 Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
Isarelnaw napui camo touk laipalah, tongpa ting taruk touh, Raameses khopui hoi a tâco awh teh Sukkoth lah a cei awh.
38 Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
Alouklouke taminaw haiyah a tawn e tu, maito hoi saringnaw pueng hoi a kâbang awh.
39 Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
Izip ram hoi a phu e tonphuenhoehe tavai a la awh teh, tonphuenhoehe a tau awh. Bangkongtetpawiteh, Izip ram hoi tang a pâlei awh dawkvah, canei kawi kârakueng mang awh hoeh.
40 Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
Isarelnaw teh Izip ram vah kum 430 touh imyin lah ao awh.
41 A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
A kum 430 akuepnae hnin dawk BAWIPA e ransanaw teh Izip ram hoi a tâco awh.
42 Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
Izip ram hoi a tâcokhai dawkvah hote tangmin teh BAWIPA hanlah a ya awh. Hatdawkvah, hote tangmin teh Isarelnaw ni pout laipalah pou a ya awh e tangmin lah ao.
43 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
BAWIPA ni Mosi hoi Aron koevah, ceitakhai pawi phunglam teh hettelah ao. Ceitakhai pawiteh alouke miphun ni cat mahoeh.
44 Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
Hateiteh, tangka hoi ran e san ni teh vuensoma hnukkhu a ca han.
45 amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
Miphun alouke hoi san lah hno e naw ni teh cat mahoeh.
46 “Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
Im buet touh dawk na ca han. A moi im alawilah na sin mahoeh. A hru hai na khoe mahoeh.
47 Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
Isarelnaw pueng ni hote pawiteh na tarawi awh han.
48 “Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
Hahoi, nangmouh koe kârayen e Jentelnaw ni BAWIPA hanlah ceitakhai pawi sak han ngai awh pawiteh, tongpanaw pueng vuensoma awh naseh. Hathnukkhu hote tami teh khoca patetlah ao dawkvah pawi kâen naseh. Vuensom ka a hoeh e teh hote pawi cat thai hoeh.
49 Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
Khocanaw hoi nangmouh koe kârayennaw hanlah phunglam buet touh dueng doeh kaawm telah BAWIPA ni Mosi hoi Aron koe a dei pouh.
50 Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
Hottelah, BAWIPA ni Mosi hoi Aron koe a dei pouh e patetlah Isarelnaw ni a sak awh.
51 A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.
Hote hnin dawk BAWIPA ni Isarelnaw a ransanaw khue hoi Izip ram hoi a tâcokhai.

< Fitowa 12 >