< Esta 7 >
1 Saboda haka sarki da Haman suka tafi cin abinci wurin sarauniya Esta.
Så kom da kongen og Haman til gjestebudet hos dronning Ester.
2 Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
Mens de satt og drakk vin, sa kongen også denne annen dag til Ester: Hvad er din bønn, dronning Ester? Den skal tilståes dig. Og hvad er ditt ønske? Var det enn halvdelen av riket, skal det opfylles.
3 Sai Sarauniya Esta ta amsa ta ce, “In na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, in kuma mai girma ya yarda, a bar ni da raina, wannan shi ne roƙona. Ka kuma sa kada a kashe mutanena, wannan ita ce bukata.
Da svarte dronning Ester: Har jeg funnet nåde for dine øine, konge, og tykkes det kongen godt, så la mitt liv bli mig gitt på min bønn, og mitt folks liv efter mitt ønske!
4 Gama an sayar da ni da mutanena don a hallaka, a karkashe mu, a kuma ƙi mu. Da a ce an sayar da mu kamar bayi maza da mata ne, da na yi shiru, domin wannan zai zama abin da bai taka kara ya karye ba, har da za a dami sarki a kai.”
For vi er solgt, både jeg og mitt folk, til å ødelegges, drepes og utryddes; var det enda bare til å være træler og trælkvinner vi var solgt, da hadde jeg tidd, men nu er vår fiende ikke i stand til å oprette kongens tap.
5 Sarki Zerzes ya tambayi Sarauniya Esta ya ce, “Wane ne shi? Ina mutumin da ya yi ƙarfin halin yin wannan karambani?”
Da sa kong Ahasverus til dronning Ester: Hvem er han, og hvor er han som har dristet sig til å gjøre så?
6 Esta ta ce, “Maƙiyi da abokin gāban, shi ne wannan mugun Haman.” Sai Haman ya tsorota a gaban sarki da sarauniya.
Ester svarte: En motstander og fiende, denne onde Haman der! Da blev Haman forferdet for kongens og dronningens åsyn.
7 Sarki ya tashi cikin fushi, ya bar ruwan inabinsa, ya fita zuwa cikin lambun fada. Amma da Haman ya gane cewa sarki ya riga ya yanke shawara a kan ƙaddararsa, ya dakata domin yă roƙi sarauniya Esta saboda ransa.
Kongen reiste sig i harme, forlot gjestebudet og gikk ut i slottshaven; men Haman blev tilbake for å be dronning Ester om sitt liv; for han skjønte at kongen hadde fast besluttet hans ulykke.
8 Sarki yana dawowa daga lambun fada zuwa babban zauren liyafan ke nan, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sarki ya tā da murya da ƙarfi ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya yayinda take tare da ni a cikin gida?” Sarki bai ma rufe baki ba, sai bayin sarki suka rufe fuskar Haman.
Da så kongen kom tilbake fra slottshaven til huset hvor gjestebudet var blitt holdt, lå Haman bøid over den benk som Ester satt på; da sa kongen: Tør han endog øve vold mot dronningen her i mitt eget hus? Ikke før var dette ord gått ut av kongens munn, før de tildekket Hamans ansikt.
9 Sai Harbona, ɗaya daga cikin bābānni masu yi wa sarki hidima ya ce, “Akwai wurin rataye mai laifi da tsayinsa ya kai ƙafa saba’in da biyar yana nan tsaye kusa da gidan Haman. Ya gyara shi ne domin a rataye Mordekai, wanda ya yi cece sarki wanda ya tone makircin masu niyya su hallaka sarki.” Sai sarki ya ce, “Ku rataye shi a kansa!”
Harbona, en av hoffmennene hos kongen, sa: Se, ved Hamans hus står det allerede en galge, femti alen høi, som han selv har latt gjøre i stand for Mordekai, han hvis ord engang var til så stort gagn for kongen. Da sa kongen: Heng ham i den!
10 Saboda haka suka rataye Haman a kan wurin rataye mai laifin da shi Haman ya shirya saboda Mordekai. Sa’an nan sarki ya huce.
Så hengte de Haman i den galge han hadde gjort i stand for Mordekai, og kongens vrede la sig.