< Esta 7 >

1 Saboda haka sarki da Haman suka tafi cin abinci wurin sarauniya Esta.
Inkosi loHamani basebesiyakudla leNdlovukazi u-Esta,
2 Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
kwathi besanatha iwayini ngalelolanga lesibili, inkosi yabuza njalo yathi, “Ndlovukazi Esta, kuyini okucelayo na? Uzakukwamukeliswa. Kuyini okucelayo na? Uzanikwa loba yini okungafika kungxenye yombuso.”
3 Sai Sarauniya Esta ta amsa ta ce, “In na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, in kuma mai girma ya yarda, a bar ni da raina, wannan shi ne roƙona. Ka kuma sa kada a kashe mutanena, wannan ita ce bukata.
INdlovukazi yaphendula yathi, “Nxa ngifumene umusa kuwe nkosi, njalo nxa inkosi kuyithokozisa, bengicelela ukuphila, yiso isicelo sami lesi.
4 Gama an sayar da ni da mutanena don a hallaka, a karkashe mu, a kuma ƙi mu. Da a ce an sayar da mu kamar bayi maza da mata ne, da na yi shiru, domin wannan zai zama abin da bai taka kara ya karye ba, har da za a dami sarki a kai.”
Ngoba mina kanye labantu bakithi sithengisiwe ukuze sichithwe njalo sibulawe ukuze singabikhona emhlabeni. Ngabe besimane sathengiswa njengezigqili zesilisa lezesifazane, bengizazithulela, ngoba akulahlupho olunje olungabangela ukuthi inkosi iphanjaniswe.”
5 Sarki Zerzes ya tambayi Sarauniya Esta ya ce, “Wane ne shi? Ina mutumin da ya yi ƙarfin halin yin wannan karambani?”
Inkosi u-Ahasuweru wathi ku-Esta iNdlovukazi, “Ngubani lowo? Ungaphi umuntu obelesibindi sokwenza into enje?”
6 Esta ta ce, “Maƙiyi da abokin gāban, shi ne wannan mugun Haman.” Sai Haman ya tsorota a gaban sarki da sarauniya.
U-Esta wathi, “Isitha lomuntu ololunya nguyenalo uHamani olomona.” UHamani wasethuthumela phambi kwenkosi lendlovukazi.
7 Sarki ya tashi cikin fushi, ya bar ruwan inabinsa, ya fita zuwa cikin lambun fada. Amma da Haman ya gane cewa sarki ya riga ya yanke shawara a kan ƙaddararsa, ya dakata domin yă roƙi sarauniya Esta saboda ransa.
Inkosi yasukuma igcwele ulaka yatshiya iwayini layo yaya phandle esivandeni sesigodlo. Kwathi uHamani ebona ukuthi inkosi yayisiyenze isinqumo ngempilo yakhe, wasala ngemuva ukuba azincengele impilo yakhe eNdlovukazini u-Esta.
8 Sarki yana dawowa daga lambun fada zuwa babban zauren liyafan ke nan, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sarki ya tā da murya da ƙarfi ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya yayinda take tare da ni a cikin gida?” Sarki bai ma rufe baki ba, sai bayin sarki suka rufe fuskar Haman.
Kwathi inkosi isiphendukile esivandeni sesigodlo ingena endlini yedili, yathola uHamani eziphosa esihlalweni lapho u-Esta ayehlezi khona. Inkosi yababaza yathi, “Kambe ungadlova indlovukazi ngikhonapha endlini na!” Kwathi ilizwi lelo liphuma emlonyeni wenkosi, bagubuzela ubuso bukaHamani.
9 Sai Harbona, ɗaya daga cikin bābānni masu yi wa sarki hidima ya ce, “Akwai wurin rataye mai laifi da tsayinsa ya kai ƙafa saba’in da biyar yana nan tsaye kusa da gidan Haman. Ya gyara shi ne domin a rataye Mordekai, wanda ya yi cece sarki wanda ya tone makircin masu niyya su hallaka sarki.” Sai sarki ya ce, “Ku rataye shi a kansa!”
Kwathi uHaribhona, omunye wabathenwa ababesebenzela inkosi wathi, “Kulensika yokulengisa abantu ephakeme okuzingalo ezingamatshumi amahlanu emiswe eduze lendlu kaHamani. Yena ubeyenzele uModekhayi, owaveza icebo elibi ukusiza inkosi.” Inkosi yathi, “Mlengiseni kuyo!”
10 Saboda haka suka rataye Haman a kan wurin rataye mai laifin da shi Haman ya shirya saboda Mordekai. Sa’an nan sarki ya huce.
Bamlengisa kuleyonsika ayeyilungisele ukulengisa uModekhayi. Ulaka lwenkosi lwaseludeda.

< Esta 7 >