< Esta 7 >

1 Saboda haka sarki da Haman suka tafi cin abinci wurin sarauniya Esta.
Da Kongen tillige med Haman var kommet til Gæstebudet hos Dronning Ester
2 Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
spurgte Kongen atter den Dag Ester, medens de sad ved Vinen: "Hvad er din Bøn, Dronning Ester? Du skal få den opfyldt. Og hvad er dit Ønske? Om det så er Halvdelen af Riget, skal det tilstås dig!"
3 Sai Sarauniya Esta ta amsa ta ce, “In na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, in kuma mai girma ya yarda, a bar ni da raina, wannan shi ne roƙona. Ka kuma sa kada a kashe mutanena, wannan ita ce bukata.
Dronning Ester svarede: "Hvis jeg har fundet Nåde for dine Øjne, Konge, og hvis Kongen synes, giv mig så mit Liv på min Bøn og giv mig mit Folk på mit Ønske;
4 Gama an sayar da ni da mutanena don a hallaka, a karkashe mu, a kuma ƙi mu. Da a ce an sayar da mu kamar bayi maza da mata ne, da na yi shiru, domin wannan zai zama abin da bai taka kara ya karye ba, har da za a dami sarki a kai.”
thi jeg og mit Folk er solgt til at udryddes, ihjelslås og tilintetgøres. Var vi endda solgt som Trælle og Trælkvinder, vilde jeg have tiet, thi så havde Ulykken ikke været stor nok til at ulejlige Kongen med!"
5 Sarki Zerzes ya tambayi Sarauniya Esta ya ce, “Wane ne shi? Ina mutumin da ya yi ƙarfin halin yin wannan karambani?”
Da svarede Kong Ahasverus Dronning Ester: "Hvem er han, og hvor er han, som har fået i Sinde at gøre dette?"
6 Esta ta ce, “Maƙiyi da abokin gāban, shi ne wannan mugun Haman.” Sai Haman ya tsorota a gaban sarki da sarauniya.
Ester svarede: En fjendsk og ildesindet Mand, den onde Haman der!" Da blev Haman slaget af Rædsel for Kongen og Dronningen.
7 Sarki ya tashi cikin fushi, ya bar ruwan inabinsa, ya fita zuwa cikin lambun fada. Amma da Haman ya gane cewa sarki ya riga ya yanke shawara a kan ƙaddararsa, ya dakata domin yă roƙi sarauniya Esta saboda ransa.
Og Kongen rejste sig i Vrede fra Gæstebudet og gik ud i Paladsets Park, men Haman blev tilbage for al bønfalde Dronning Ester om sit Liv; thi han mærkede, at det var Kongens faste Vilje at styrte ham i Ulykke.
8 Sarki yana dawowa daga lambun fada zuwa babban zauren liyafan ke nan, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sarki ya tā da murya da ƙarfi ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya yayinda take tare da ni a cikin gida?” Sarki bai ma rufe baki ba, sai bayin sarki suka rufe fuskar Haman.
Da Kongen kom tilbage fra Paladsets Park til Gæstebudsalen, havde Haman netop kastet sig ned over Divanen, som Ester lå på. Så sagde Kongen: "Vil han oven i Købet øve Vold imod Dronningen her i Huset i min Nærværelse!" Næppe var det Ord udgået af Kongens Mund, før man tilhyllede Hamans Ansigt;
9 Sai Harbona, ɗaya daga cikin bābānni masu yi wa sarki hidima ya ce, “Akwai wurin rataye mai laifi da tsayinsa ya kai ƙafa saba’in da biyar yana nan tsaye kusa da gidan Haman. Ya gyara shi ne domin a rataye Mordekai, wanda ya yi cece sarki wanda ya tone makircin masu niyya su hallaka sarki.” Sai sarki ya ce, “Ku rataye shi a kansa!”
og Harbona, en af Hofmændene, der stod i Kongens Tjeneste, sagde: "Ved Hamans Hus står allerede den halvtredsindstyve Alen høje Galge, som Haman har ladet rejse til Mordokaj, hvis Ord dog var Kongen til Gavn!" Da sagde Kongen: "Hæng ham i den!"
10 Saboda haka suka rataye Haman a kan wurin rataye mai laifin da shi Haman ya shirya saboda Mordekai. Sa’an nan sarki ya huce.
Og de hængte Haman i den Galge, han havde rejst til Mordokaj. Så lagde Kongens Vrede sig.

< Esta 7 >