< Esta 7 >
1 Saboda haka sarki da Haman suka tafi cin abinci wurin sarauniya Esta.
Der Kongen og Haman vare komne at drikke hos Dronning Esther,
2 Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
da sagde Kongen til Esther ogsaa anden Dag under Gæstebudet ved Vinen: Hvad er din Bøn, Dronning Esther? og det skal gives dig; og hvad er din Begæring? var det indtil Halvdelen af Riget, da skal det ske.
3 Sai Sarauniya Esta ta amsa ta ce, “In na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, in kuma mai girma ya yarda, a bar ni da raina, wannan shi ne roƙona. Ka kuma sa kada a kashe mutanena, wannan ita ce bukata.
Og Dronning Esther svarede og sagde: Dersom jeg har fundet Naade for dine Øjne, o Konge! og dersom det synes Kongen godt, da lad der gives mig mit Liv for min Bøns Skyld og mit Folk for min Begærings Skyld!
4 Gama an sayar da ni da mutanena don a hallaka, a karkashe mu, a kuma ƙi mu. Da a ce an sayar da mu kamar bayi maza da mata ne, da na yi shiru, domin wannan zai zama abin da bai taka kara ya karye ba, har da za a dami sarki a kai.”
Thi vi ere solgte, jeg og mit Folk, til at ødelægges, at ihjelslaaes og at udryddes; og vare vi endda solgte til Tjenere og til Tjenestepiger, saa vilde jeg have tiet; thi Fjenden kan ikke oprette Kongen den Skade.
5 Sarki Zerzes ya tambayi Sarauniya Esta ya ce, “Wane ne shi? Ina mutumin da ya yi ƙarfin halin yin wannan karambani?”
Da svarede Kong Ahasverus og sagde til Dronning Esther: Hvo er den, eller hvor er han, som har taget sig for i sit Hjerte at gøre saaledes?
6 Esta ta ce, “Maƙiyi da abokin gāban, shi ne wannan mugun Haman.” Sai Haman ya tsorota a gaban sarki da sarauniya.
Og Esther sagde: Den Mand, den Modstander og Fjende, er denne onde Haman; og Haman blev forfærdet for Kongens og Dronningens Ansigt.
7 Sarki ya tashi cikin fushi, ya bar ruwan inabinsa, ya fita zuwa cikin lambun fada. Amma da Haman ya gane cewa sarki ya riga ya yanke shawara a kan ƙaddararsa, ya dakata domin yă roƙi sarauniya Esta saboda ransa.
Og Kongen stod op i sin Harme fra Gæstebudet og Vinen og gik ned i Haven ved Paladset; og Haman blev staaende for at bede Dronning Esther om sit Liv; thi han saa, at der var besluttet en Ulykke over ham af Kongen.
8 Sarki yana dawowa daga lambun fada zuwa babban zauren liyafan ke nan, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sarki ya tā da murya da ƙarfi ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya yayinda take tare da ni a cikin gida?” Sarki bai ma rufe baki ba, sai bayin sarki suka rufe fuskar Haman.
Og Kongen kom tilbage fra Haven ved Paladset til Huset, hvor der havde været Gæstebud med Vin; men Haman var segnet ned over Bænken, som Esther sad paa; da sagde Kongen: Vil han og øve Vold imod Dronningen hos mig i Huset? Ordet var udgaaet af Kongens Mund, og de tilhyllede Hamans Ansigt.
9 Sai Harbona, ɗaya daga cikin bābānni masu yi wa sarki hidima ya ce, “Akwai wurin rataye mai laifi da tsayinsa ya kai ƙafa saba’in da biyar yana nan tsaye kusa da gidan Haman. Ya gyara shi ne domin a rataye Mordekai, wanda ya yi cece sarki wanda ya tone makircin masu niyya su hallaka sarki.” Sai sarki ya ce, “Ku rataye shi a kansa!”
Og Harbona, en af Kammertjenerne, som stode for Kongens Ansigt, sagde: Se, der staar ogsaa Træet, som Haman har lavet til for Mardokaj, der talte, hvad der var godt for Kongen, ved Hamans Hus, halvtredsindstyve Alen højt; da sagde Kongen: Hænger ham derpaa!
10 Saboda haka suka rataye Haman a kan wurin rataye mai laifin da shi Haman ya shirya saboda Mordekai. Sa’an nan sarki ya huce.
Saa hængte de Haman paa Træet, som han havde ladet lave til for Mardokaj; og Kongens Harme stilledes.