< Afisawa 4 >
1 A matsayina na ɗan kurkuku saboda Ubangiji, ina roƙonku ku yi rayuwar da ta dace da kiran da aka yi muku.
I, therefore, as the prisoner for the Lord, urge you to walk worthily of the calling by which you were called.
2 Kullum ku kasance masu sauƙinkai da kuma hankali; ku zama masu haƙuri, kuna jimrewa da juna cikin ƙauna.
I urge you to live with great humility and gentleness and patience, putting up with one another in love.
3 Ku yi ƙoƙari sosai ku kiyaye zaman ɗayan nan da Ruhu ya ba ku, ku yi haka ta wurin zaman lafiya da juna.
Do your best to keep the unity of the Spirit in the bond of peace.
4 Dukanku jiki ɗaya ne, kuna kuma da Ruhu guda. An ba ku bege guda sa’ad da aka kira ku.
There is one body and one Spirit, just as also you were called in one certain hope of your calling.
5 Ubangiji ɗaya, bangaskiya ɗaya, baftisma kuma ɗaya,
And there is one Lord, one faith, one baptism,
6 Allah ɗaya Uban duka, wanda yake a bisa duka, ta wurin duka, a cikin duka kuma.
and one God and Father of all, who is over all and through all and in all.
7 Amma ga kowannenmu an ba da alheri bisa ga yadda Kiristi ya rarraba.
To each one of us grace has been given according to the measure of the gift of Christ.
8 Shi ya sa aka ce, “Sa’ad da ya hau sama, ya bi da kamammu kamar tawagarsa ya kuma ba da baye-baye ga mutane.”
It is as scripture says: “When he ascended to the heights, he led the captives into captivity, and he gave gifts to the people.”
9 (Me ake nufin da “ya hau,” in ba cewa dā ya sauka can ƙarƙashin ƙasa ba?
What is the meaning of “He ascended,” except that he also descended into the lower regions of the earth?
10 Shi wannan da ya sauka ɗin, shi ne kuma ya hau zuwa can sama, kai, gaba da sammai, don mulkinsa yă cika duniya gaba ɗaya.)
He who descended is the same person who also ascended far above all the heavens, that he might fill all things.
11 Saboda haka Kiristi kansa ya ba wa waɗansu baiwa su zama manzanni, waɗansu su zama annabawa, waɗansu su zama masu wa’azi, waɗansu kuma su zama fastoci, da kuma malamai.
Christ gave some to be apostles, some as prophets, some as evangelists, and some as pastors and teachers.
12 Ya yi haka don yă shirya mutanensa saboda ayyukan hidima, don a gina jikin Kiristi.
He gave these offices to equip the saints for the work of service, for the building up of the body of Christ.
13 Wannan zai ci gaba har sai mun zama ɗaya a cikin bangaskiya da kuma ta wurin fahimtarmu na Ɗan Allah. Sa’an nan za mu zama balagaggu, kamar yadda Kiristi yake, mu kuma zama gaba ɗaya cikakku kamar sa.
He continues to build up his body until we all reach the unity of faith and knowledge of the Son of God, and that we become mature and so reach the measure of the fullness of Christ.
14 An yi wannan kuwa don kada mu koma zama kamar yara, muna ta canja zukatanmu game da abin da muka gaskata don kawai wani ya faɗa mana wani abu dabam, ko domin wani ya yi wayo ya ruɗe mu, ya sa ƙarya ta zama kamar gaskiya.
Christ builds us up so that we should no longer be children who are tossed back and forth by the waves, and carried away by every wind of teaching and by the trickery of people in their deceitful schemes.
15 Ya kamata kullum ƙauna tă sa mu faɗa gaskiya. Ta haka za mu yi girma a kowace hanya, mu kuma zama kamar Kiristi, wanda yake kan
Instead, speaking the truth in love, we are to grow up in every way into him who is the head, that is, Christ.
16 dukan jiki. Shi ne ya haɗe jiki duka, ya kuma sa dukan gaɓoɓin jiki suna aiki daidai, yayinda kowace gaɓa take aikinta cikin ƙauna.
Christ builds the whole body, and it is joined and held together by every supporting ligament, and when each part works together, that makes the body grow so that it builds itself up in love.
17 To, ina dai faɗa muku, ina kuma nace faɗa muku a cikin Ubangiji, cewa kada ku ci gaba da yin rayuwa kamar yadda Al’ummai suke yi, masu banzan tunani.
Therefore, I say and insist on this in the Lord, that you must no longer live as the Gentiles live, in the futility of their minds.
18 Suna a cikin duhu a fahimtarsu, kuma a rabe suke daga ran Allah saboda jahilcin da yake cikinsu ta dalilin taurarewar zukatansu.
They are darkened in their understanding, alienated from the life of God because of the ignorance that is in them, because of the hardness of their hearts.
19 Ba sa damu da wani abu ko mai kyau ko marar kyau. Rayukansu sun cika da kowace irin ƙazanta da haɗama.
They have no shame and have handed themselves over to sensuality, and they are continually practicing every kind of impurity.
20 Amma ba abin da aka koya muku ke nan ba sa’ad da kuka zo ga sanin Kiristi.
But that is not how you learned about Christ.
21 Da yake kun ji duka game da shi, kuka kuma koyi gaskiyar da take cikin Yesu,
I assume that you have heard about him, and that you were taught in him, as the truth is in Jesus.
22 sai ku tuɓe tsohon mutumin nan naku da kuma rayuwarku ta dā, wadda take lalacewa saboda sha’awace-sha’awacen da suke ruɗe ku.
You were taught to put off what belongs to your former manner of life, to put off the old man. It is the old man that is corrupt because of its deceitful desires.
23 A maimakon haka, bari Ruhu yă sabunta tunaninku da kuma halayenku.
You were taught to be renewed in the spirit of your minds,
24 Ku sanya sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah, halin nan kuwa, yă bayyana cikin adalci, da zaman tsarki.
and to put on the new man that is created in the image of God—in true righteousness and holiness.
25 Saboda haka dole kowannenku yă bar yin ƙarya, yă kuma riƙa faɗa wa maƙwabcinsa gaskiya, gama dukanmu gaɓoɓi jiki ɗaya ne.
Therefore, get rid of lies, and let each one of you speak truth with his neighbor, because we are members of one another.
26 “Cikin fushinku kada ku yi zunubi.” Kada ku bar rana ta fāɗi kuna fushi,
Be angry and do not sin. Do not let the sun go down on your anger.
27 kada kuma ku ba wa Iblis dama.
Do not give an opportunity to the devil.
28 Duk wanda yake sata, sai yă daina sata, dole kuma yă yi aiki, yă yi wani abu mai amfani da hannuwansa, don yă sami abin da zai iya raba da masu bukata.
The one who had been stealing must steal no longer. He must labor, doing useful work with his hands, so that he may have something to share with those who are in need.
29 Kada wata ƙazamar magana ta fita daga bakunanku, sai dai abin da yake da amfani don gina waɗansu bisa ga bukatunsu. Ta haka maganarku za tă zama da amfani ga masu jinta.
Do not let any filthy talk come out of your mouth. Use only words that are helpful for building others up, according to their needs, that your words would be helpful to those who hear you.
30 Kada kuma ku ɓata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai, wanda da shi aka hatimce ku da shi don ranar fansa.
And do not grieve the Holy Spirit of God, for it is by him that you were sealed for the day of redemption.
31 Ku rabu da kowane irin ɗacin rai, haushi da hasala, faɗa da ɓata suna, ku rabu da kowace irin ƙeta.
Put away all bitterness, rage, anger, quarreling, and insults, along with every kind of evil.
32 Ku yi alheri, ku kuma ji tausayin juna, kuna gafarta wa juna, kamar yadda a cikin Kiristi, Allah ya gafarta muku.
Be kind to each other, tenderhearted, forgiving one another, just as God in Christ forgave you.