< 2 Korintiyawa 11 >
1 Ina fata za ku yi haƙuri da’yar wautata. Amma, ai, kun riga kun yi haƙuri.
I wish that you could put up with me in some foolishness. But you are indeed putting up with me!
2 Ina kishinku da kishi irin na Allah. Na yi muku alkawarin aure ga miji ɗaya, Kiristi, domin in miƙa ku a gare shi kamar budurwa zalla.
For I am jealous about you. I have a godly jealousy for you, since I promised you in marriage to one husband. I promised to present you as a pure virgin to Christ.
3 Sai dai ina tsoro kada yă zama, kamar yadda maciji ya yaudari Hawwa’u da makircinsa, ku ma a bauɗar da hankalinku daga sahihiyar biyayya amintacciya ga Kiristi.
But I am afraid that somehow, as the serpent deceived Eve by his craftiness, your thoughts might be led astray away from a sincere and pure devotion to Christ.
4 Gama in wani ya zo wurinku yana wa’azin wani Yesu dabam da wanda muka yi wa’azinsa, ko kuma in kun karɓi wani ruhu dabam da wanda kuka karɓa, ko wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, ya nuna kun yarda da su ke nan cikin sauƙinkai.
For suppose that someone comes and proclaims another Jesus than the one we preached. Or suppose that you receive a different spirit than what you received. Or suppose that you receive a different gospel than the one you received. You put up with these things well enough!
5 Amma a ganina waɗancan da kuke ce da su “manyan manzanni” ba su fi ni da wani abu ba.
For I think that I am not in the least inferior to those so-called super-apostles.
6 Mai yiwuwa ni ba horarre ba ne a magana, amma ina da sani. Mun kuwa bayyana muku wannan a sarari, ta kowace hanya.
But even if I am untrained in giving speeches, I am not untrained in knowledge. In every way and in all things we have made this known to you.
7 Laifi ke nan ne na yi da na ƙasƙantar da kaina, don a ɗaga ku zuwa babban matsayi ta wurin yin muku wa’azin bisharar Allah kyauta?
Did I sin by humbling myself so you might be exalted? For I freely preached the gospel of God to you.
8 Na yi wa waɗansu ikkilisiyoyi ƙwace ta wurin karɓar taimako daga wurinsu, domin in yi muku hidima.
I robbed other churches by accepting support from them so that I could serve you.
9 Sa’ad da nake tare da ku kuma nake zaman rashi, ban nawaita wa kowa ba, gama’yan’uwan da suka zo daga Makidoniya sun biya bukata. Na kiyaye kaina daga nawaita muku ta kowace hanya, zan kuma ci gaba da yin haka.
When I was with you and I was in need, I did not burden anyone. For my needs were met by the brothers who came from Macedonia. In everything I have kept myself from being a burden to you, and I will continue to do that.
10 Ba shakka, kamar yadda gaskiyar Kiristi take a cikina, babu wani a yankunan Akayya da zai iya hana yin taƙaman nan tawa.
As the truth of Christ is in me, this boasting of mine will not be silenced in the parts of Achaia.
11 Don me? Don ba na ƙaunar ku ne? Allah dai ya sani ina ƙaunarku!
Why? Because I do not love you? God knows.
12 Zan kuma ci gaba da yin abin da nake yi, domin in toshe kafar mutanen nan da suke fariya, suna nema mu daidaita da su.
And what I do I will keep doing, in order that I may take away the claim for criticizing me and the claim for which they want to boast—that they are found to be doing the same work that we are doing.
13 Gama irin waɗannan mutane manzannin ƙarya ne, ma’aikata ne masu ruɗi, sun ɓad da kamanni kamar su manzannin Kiristi ne.
For such people are false apostles and deceitful workers. They disguise themselves as apostles of Christ.
14 Ba abin mamaki ba ne, gama Shaiɗan kansa ma yana ɓad da kamanni kamar shi mala’ikan haske ne.
And this is no surprise, for even Satan disguises himself as an angel of light.
15 Don haka, ba abin mamaki ba ne, in bayin Shaiɗan sun ɓad da kamanni kamar su bayin adalci ne. A ƙarshe, za a sāka musu gwargwadon ayyukansu.
It is no great surprise if his servants also disguise themselves as servants of righteousness. Their fate will be what their deeds deserve.
16 Ina sāke faɗa, kada wani yă ɗauka ni wawa ne. Amma in kun ɗauke ni haka, to, sai ku karɓe ni kamar yadda kuke karɓan wawa, domin in ɗan in yi taƙama.
I say again: Let no one think I am a fool. But if you do, receive me as a fool so I may boast a little.
17 A wannan taƙamata ba na magana yadda Ubangiji zai yi ba ne, sai dai magana ce irin ta wawa.
What I am saying with this boastful confidence—I am not talking the way the Lord would—I am saying as a fool.
18 Da yake mutane da yawa suna taƙama irin ta duniya, ni ma haka zan yi.
Since many people boast according to the flesh, I will also boast.
19 Ku kam kuna da wayo sosai, har kuna jimre wa wawaye da murna!
For you gladly put up with fools. You are wise yourselves!
20 Gaskiyar ita ce, kuna haƙuri da duk wanda ya sa ku bauta ko ya cuce ku ko ya more ku ko ya nuna muku isa ko kuma ya mare ku a fuska.
For you put up with someone if he enslaves you, if he consumes you, if he takes advantage of you, if he considers himself better than you, or if he slaps you in the face.
21 Ina jin kunya in ce mun nuna kāsawa da ba mu yi waɗannan abubuwan ba! Abin da wani yake da ƙarfin hali yin taƙama a kai, shi ne ni ma nake ƙarfin hali yin taƙama a kai. Ina magana kamar wawa ne.
I will say to our shame that we were too weak to do that. Yet if anyone boasts—I am speaking like a fool—I too will boast.
22 In su Ibraniyawa ne, ni ma haka. In su Isra’ilawa ne, ni ma haka. In su zuriyar Ibrahim ne, ni ma haka.
Are they Hebrews? So am I. Are they Israelites? So am I. Are they descendants of Abraham? So am I.
23 In su bayin Kiristi ne, ni na fi su ma, ina magana kamar ruɗaɗɗe ne fa! Ai, na fi su shan fama ƙwarai da gaske, da shan dauri, na sha dūka marar iyaka, na sha hatsarin mutuwa iri-iri.
Are they servants of Christ? (I speak as though I were out of my mind.) I am more. I have been in even more hard work, in far more prisons, in beatings beyond measure, in facing many dangers of death.
24 Sau biyar Yahudawa suka yi mini bulala arba’in ɗaya babu.
From Jews I received five times the “forty lashes minus one.”
25 Sau uku aka bulale ni da bulalar ƙarfe, sau ɗaya aka jajjefe ni da duwatsu, sau uku jirgin ruwa ya ragargaje ina ciki, na kwana na kuma yini ruwan teku yana tafiya da ni.
Three times I was beaten with rods. Once I was stoned. Three times I was shipwrecked. I have spent a night and a day on the open sea.
26 Na yi tafiye-tafiye da yawa, na sha hatsari a koguna, na sha hatsarin’yan fashi, na sha hatsari a hannun kabilarmu, na sha hatsari a hannun al’ummai, na sha hatsari a birane, na sha hatsari a jeji, na sha hatsari a teku, na kuma sha hatsarin’yan’uwa na ƙarya.
I have been on frequent journeys, in danger from rivers, in danger from robbers, in danger from my own people, in danger from the Gentiles, in danger in the city, in danger in the wilderness, in danger at sea, in danger from false brothers.
27 Na yi fama, na shan wuya, ga kuma rashin barci sau da yawa. Na san abin da ake nufin da jin yunwa da ƙishirwa, sau da yawa kuwa na kasance da rashin abinci, na sha sanyi da zaman tsirara.
I have been at hard work and in hardship, in many sleepless nights, in hunger and thirst, often in fasting, in cold and nakedness.
28 Ban da waɗannan abubuwa, kowace rana ina ɗauke da nauyin kula da dukan ikkilisiyoyi.
Apart from everything else, there is the daily pressure on me of my anxiety for all the churches.
29 Wane ne ya rasa ƙarfi, da ban ji shi a jikina ba? Wane ne ya fāɗi cikin zunubi, da ban ji zafin wannan ba?
Who is weak, and I am not weak? Who has been caused to stumble, and I do not burn?
30 In ma lalle ne in yi taƙama, to, sai in yi taƙama da abubuwan da suka nuna rashin ƙarfina.
If I must boast, I will boast about what shows my weaknesses.
31 Allah Uban Ubangiji Yesu Kiristi, wanda yabo ta tabbata a gare shi har abada, ya san cewa ba ƙarya nake yi ba. (aiōn )
The God and Father of the Lord Jesus, the one who is praised forever, knows that I am not lying! (aiōn )
32 A Damaskus, gwamnan da yake ƙarƙashin Sarki Aretas, ya sa tsare ƙofofin birnin Damaskus, don yă kama ni.
At Damascus, the governor under King Aretas was guarding the city of Damascus to arrest me.
33 Amma aka saukar da ni cikin kwando ta tagar katanga, na kuɓuce masa.
But I was lowered in a basket through a window in the wall, and I escaped from his hands.