< Maimaitawar Shari’a 5 >
1 Musa ya tattara dukan Isra’ila ya ce, Ku ji, ya Isra’ila, ƙa’idodi da dokokin da na furta a kunnuwanku a yau. Ku koye su, ku kuma tabbata kun bi su.
Musa bütün İsrailliler'i bir araya toplayarak şöyle dedi: “Ey İsrail, bugün size bildireceğim kurallara, ilkelere kulak verin! Onları öğrenin ve onlara uymaya dikkat edin!
2 Ubangiji Allahnmu ya yi alkawari da mu a Horeb.
Tanrımız RAB Horev Dağı'nda bizimle bir antlaşma yaptı.
3 Ba da kakanninmu ba ne Ubangiji ya yi wannan alkawari, amma da mu ne, da dukanmu waɗanda muke da rai a yau.
RAB bu antlaşmayı atalarımızla değil, bizimle, bugün burada sağ kalan hepimizle yaptı.
4 Ubangiji ya yi magana fuska da fuska da ku daga wuta a kan dutse.
RAB dağda ateşin içinden sizinle yüz yüze konuştu.
5 (A wannan lokaci na tsaya tsakanin Ubangiji da ku, don in furta muku maganar Ubangiji, domin kun ji tsoron wutar, ba ku kuwa hau dutsen ba.) Ya ce,
O zaman RAB'bin sözünü size bildirmek için RAB ile sizin aranızda durdum. Çünkü siz ateşten korkup dağa çıkmadınız. RAB şöyle seslendi:
6 “Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
“‘Seni Mısır'dan, köle olduğun ülkeden çıkaran Tanrın RAB benim.
7 “Ba za ka kasance da waɗansu alloli a gabana ba.
“‘Benden başka tanrın olmayacak.
8 Ba za ka yi wa kanka gunki, ko wata siffar abin da take a sama a bisa, ko siffar abin da yake a duniya a ƙasa, ko siffar abin da yake a cikin ruwa a ƙarƙashin ƙasa ba.
“‘Kendine yukarıda gökyüzünde, aşağıda yeryüzünde ya da yer altındaki sularda yaşayan herhangi bir canlıya benzer put yapmayacaksın.
9 Ba za ka rusuna musu, ko ka yi musu sujada ba. Gama Ni, Ubangiji Allahnka, Allah ne mai kishi, nakan hukunta’ya’ya saboda zunuban iyaye har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni.
Putların önünde eğilmeyecek, onlara tapmayacaksın. Çünkü ben, Tanrın RAB, kıskanç bir Tanrı'yım. Benden nefret edenin babasının işlediği suçun hesabını çocuklarından, üçüncü, dördüncü kuşaklardan sorarım.
10 Amma nakan nuna ƙauna ga dubban tsararraki na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye dokokina.
Ama beni seven, buyruklarıma uyan binlerce kuşağa sevgi gösteririm.
11 Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai ba wa duk mai yin amfani da sunansa a banza laifi.
“‘Tanrın RAB'bin adını boş yere ağzına almayacaksın. Çünkü RAB, adını boş yere ağzına alanları cezasız bırakmayacaktır.
12 Ka kiyaye ranar Asabbaci ta wurin kiyaye ta da tsarki, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka.
“‘Tanrın RAB'bin buyruğu uyarınca Şabat Günü'nü tut ve kutsal say.
13 Kwanaki shida za ka yi aiki, ka kuma yi dukan aikinka,
Altı gün çalışacak, bütün işlerini yapacaksın.
14 amma rana ta bakwai, Asabbaci ne ga Ubangiji Allahnka. A kanta ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawanka, ko baiwarka, ko saniyarka, ko jakinka, ko wani daga dabbobinka, ko baƙo a ƙofofinka, don bayinka maza da mata su ma su huta, kamar ka.
Ama yedinci gün bana, Tanrın RAB'be Şabat Günü olarak adanmıştır. O gün sen, oğlun, kızın, erkek ve kadın kölen, öküzün, eşeğin ya da herhangi bir hayvanın, aranızdaki yabancılar dahil, hiçbir iş yapmayacaksınız. Öyle ki, senin gibi erkek ve kadın kölelerin de dinlensinler.
15 Ka tuna fa, dā kai bawa ne a ƙasar Masar amma Ubangiji Allahnka ya fitar da kai daga can da iko da kuma ƙarfi. Saboda haka Ubangiji Allahnka ya umarce ka ka kiyaye ranar Asabbaci.
Mısır'da köle olduğunu ve Tanrın RAB'bin seni oradan güçlü ve kudretli eliyle çıkardığını anımsayacaksın. Tanrın RAB bu yüzden Şabat Günü'nü tutmanı buyurdu.
16 Ka ba da girma ga mahaifinka da mahaifiyarka, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka, don ka yi tsawon rai, ka kuma sami zaman lafiya a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
“‘Tanrın RAB'bin buyruğu uyarınca annene babana saygı göster. Öyle ki, ömrün uzun olsun ve Tanrın RAB'bin sana vereceği ülkede üzerine iyilik gelsin.
20 Kada ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka.
“‘Komşuna karşı yalan yere tanıklık etmeyeceksin.
21 Kada ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka. Kada kuma ka yi sha’awar gidan maƙwabcinka, ko gonarsa, ko bayinsa maza da mata, ko saniyarka, ko jakinsa, ko dai wani abin da yake na maƙwabtanka.”
“‘Komşunun karısına kötü gözle bakmayacaksın. Komşunun evine, tarlasına, erkek ve kadın kölesine, öküzüne, eşeğine, hiçbir şeyine göz dikmeyeceksin.’
22 Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya furta da babbar murya ga taronku gaba ɗaya, a can dutse ta tsakiyar wuta, girgije da kuma baƙin duhu; bai kuma ƙara kome ba. Sa’an nan ya rubuta su a kan alluna biyu na dutse, ya kuma ba ni su.
“RAB bu sözleri dağda ateşin, bulutun, koyu karanlığın içinden bütün topluluğunuza yüksek sesle söyledi. Başka bir şey eklemedi. Sonra bunları iki taş levha üstüne yazıp bana verdi.
23 Sa’ad da kuka ji muryar daga duhu, yayinda dutsen yana cin wuta, dukan manyan kabilanku da dattawanku suka zo wurina.
“Dağ alev alev yanarken karanlığın içinden sesi duyduğunuzda bütün oymak başlarınız ve ileri gelenlerinizle bana yaklaştınız.
24 Kuka kuma ce, “Ubangiji Allahnmu ya nuna mana ɗaukakarsa da zatinsa, mun kuma ji muryarsa a tsakiyar wutar. A yau mun ga cewa mutum zai iya rayu idan ma Allah ya yi magana da shi.
‘Tanrımız RAB bize yüceliğini ve büyüklüğünü gösterdi’ dediniz, ‘Ateşin içinden sesini duyduk. Bugün Tanrı'nın insanla konuştuğunu ve insanın ölmediğini gördük.
25 Amma yanzu, don me za mu mutu? Wannan wuta mai girma za tă cinye mu, za mu kuwa mutu in muka ci gaba da jin muryar Ubangiji Allahnmu.
Neden şimdi ölelim? Bu büyük ateş bizi yakıp yok edecek. Tanrımız RAB'bin sesini bir daha duyarsak öleceğiz.
26 Gama wanda ɗan adam ne ya taɓa jin muryar Allah mai rai yana magana daga wuta, kamar yadda muka ji, ya kuma tsira?
Ateşin içinden seslenen, yaşayan Tanrı'nın sesini bizim gibi duyup da sağ kalan var mı?
27 Kai, ka matsa kusa, ka saurara ga dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa. Sa’an nan ka faɗa mana dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa maka. Za mu saurara, mu kuma yi biyayya.”
Sen git, Tanrımız RAB'bin söyleyeceklerini dinle. Sonra Tanrımız RAB'bin bütün söylediklerini bize anlat. Biz de kulak verip uyacağız.’
28 Ubangiji ya ji ku, sa’ad da kuka yi magana da ni, sai Ubangiji ya ce mini, “Na ji abin da wannan mutane suka faɗa maka. Abin da suka faɗa daidai ne.
“RAB benimle yaptığınız konuşmayı duyunca, şöyle dedi: ‘Bu halkın sana neler söylediğini duydum. Bütün söyledikleri doğrudur.
29 Kash, da a ce zukatansu za su zama masu tsorona, su kuma kiyaye dukan dokokina kullum mana, saboda kome yă zama da lafiya gare su, da kuma’ya’yansu har abada!
Keşke benden korksalardı ve bütün buyruklarıma uymak için her zaman yürekten istekli olsalardı! O zaman kendilerine ve çocuklarına sürekli iyilik gelirdi.
30 “Je, ka faɗa musu su koma tentunansu.
“‘Git, çadırlarına dönmelerini söyle.
31 Kai kuwa ka tsaya a nan tare da ni saboda in ba ka umarnai, ƙa’idodi da kuma dokoki duka, da za ka koya musu don su bi a ƙasar da nake ba su, su mallaka.”
Ama sen burada yanımda dur. Sana bütün buyrukları, kuralları, ilkeleri vereceğim. Bunları halka sen öğreteceksin. Öyle ki, mülk edinmek için kendilerine vereceğim ülkede hepsine uysunlar.’
32 Sai ku yi hankali don ku yi abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku; kada ku juya dama ko hagu.
“Tanrınız RAB'bin size buyurduklarına uymaya özen gösterin. Onlardan sağa sola sapmayın.
33 Ku yi tafiya cikin dukan hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, saboda ku zauna, ku yi nasara, ku kuma yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.
Tanrınız RAB'bin size buyurduğu yollarda yürüyün. Öyle ki, mülk edineceğiniz ülkede sağ kalasınız, başarılı ve uzun ömürlü olasınız.”