< Maimaitawar Shari’a 34 >

1 Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
Alors Moïse monta des campagnes de Moab sur la montagne de Nébo, au sommet de la colline qui est vis-à-vis de Jéricho, et l'Eternel lui fit voir tout le pays, depuis Galaad jusques à Dan,
2 da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
Avec tout [le pays] de Nephthali, et le pays d'Ephraïm et de Manassé, et tout le pays de Juda, jusqu'à la mer Occidentale;
3 da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
Et le Midi, et la campagne de la plaine de Jérico, la ville des palmes; jusqu'à Tsohar.
4 Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
Et l'Eternel lui dit: C'est ici le pays dont j'ai juré à Abraham, à Isaac, et à Jacob, en disant: Je le donnerai à ta postérité; je te l'ai fait voir de tes yeux; mais tu n'y entreras point.
5 Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
Ainsi Moïse, serviteur de l'Eternel, mourut là au pays de Moab, selon le commandement de l'Eternel.
6 Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
Et il l'ensevelit dans la vallée, au pays de Moab, vis-à-vis de Beth-Péhor; et personne n'a connu son sépulcre jusqu'à aujourd'hui.
7 Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
Or Moïse était âgé de six vingts ans quand il mourut; sa vue n'était point diminuée, et sa vigueur n'était point passée.
8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
Et les enfants d'Israël pleurèrent Moïse trente jours dans les campagnes de Moab, et ainsi les jours des pleurs du deuil de Moïse furent accomplis.
9 To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
Et Josué, fils de Nun, fut rempli de l'Esprit de sagesse, parce que Moïse lui avait imposé les mains; et les enfants d'Israël lui obéirent, et firent ainsi que l'Eternel avait commandé à Moïse.
10 Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
Et il ne s'est jamais levé en Israël de Prophète comme Moïse, qui ait connu l'Eternel face à face;
11 wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
Selon tous les signes et les miracles que l'Eternel l'envoya faire au pays d'Egypte, devant Pharaon, et tous ses serviteurs, et tout son pays;
12 Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.
Selon toute cette main forte, et toutes ces grandes œuvres redoutables, que Moïse fit à la vue de tout Israël.

< Maimaitawar Shari’a 34 >