< Maimaitawar Shari’a 33 >

1 Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
Or c'est ici la bénédiction dont Moïse, homme de Dieu, bénit les enfants d'Israël avant sa mort.
2 Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
Il dit donc: L'Eternel est venu de Sinaï, et s'est levé à eux en Séhir; il leur a resplendi de la montagne de Paran, et il est sorti d'entre les dix milliers des Saints, et de sa dextre le feu de la Loi est sorti vers eux.
3 Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
Et même il aime les peuples, tous ses Saints [sont] en ta main; et ils se sont tenus à tes pieds pour recevoir tes paroles.
4 dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
Moïse nous a donné la Loi, qui est l'héritage de l'assemblée de Jacob;
5 Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
Et il a été Roi entre les hommes droits, quand les chefs du peuple se sont assemblés, avec les Tribus d'Israël.
6 “Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
Que RUBEN vive, et qu'il ne meure point, encore que ses hommes soient en petit nombre.
7 Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
Et c'est ici ce que [Moïse] dit pour JUDA; Ô Eternel! écoute la voix de Juda, et le ramène vers son peuple; que ses mains lui suffisent, et que tu lui sois en aide contre ses ennemis.
8 Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
Il dit aussi touchant LEVI: Tes Thummims et tes Urims sont à l'homme qui est ton bien-aimé, que tu as éprouvé en Massa, [et] contre lequel tu t'es querellé aux eaux de Mériba.
9 Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
C'est lui qui dit de son père et de sa mère: Je ne l'ai point vu; et qui n'a point connu ses frères, et n'a point aussi connu ses enfants; car ils ont gardé tes paroles, et ils garderont ton alliance.
10 Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
Ils enseigneront tes ordonnances à Jacob, et ta Loi à Israël, ils mettront le parfum en tes narines, et tout Sacrifice qui se consume entièrement par le feu sur ton autel.
11 Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
Ô Eternel! bénis ses troupes, et que l'œuvre de ses mains te soit agréable. Transperce les reins de ceux qui s'élèvent contre lui, et de ceux qui le haïssent, aussitôt qu'ils se seront élevés.
12 Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
Il dit touchant BENJAMIN: Le bien-aimé de l'Eternel habitera sûrement avec lui; il le couvrira tout le jour, et se tiendra entre ses épaules.
13 Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
Et il dit touchant JOSEPH: Son pays est béni par l'Eternel, de ce qui est le plus exquis aux cieux, de la rosée, et de l'abîme qui est en bas;
14 da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
Et de ce qu'il y a de plus exquis entre les choses que le soleil fait produire, et de ce qui est le plus excellent entre les choses que la lune fait produire;
15 da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
Et du coupeau des montagnes anciennes, et de ce qu'il y a de plus exquis sur les coteaux d'éternité;
16 Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
Et de ce qu'il y a de plus exquis sur la terre, et de son abondance; et que la bienveillance de celui qui se tenait au buisson vienne sur la tête de Joseph, sur le sommet, [dis-je], de la tête du Nazarien d'entre ses frères.
17 Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
Sa beauté est comme d'un premier-né de ses taureaux, et ses cornes comme les cornes d'une licorne; il heurtera avec elles tous les peuples jusqu'aux bouts de la terre. Ce sont les dix milliers d'Ephraïm, et ce sont les milliers de Manassé.
18 Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
Il dit aussi touchant ZABULON: Réjouis-toi, Zabulon, en ta sortie; et toi ISSACAR dans tes tentes.
19 Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
Ils appelleront les peuples en la montagne, ils offriront là des sacrifices de justice; car ils suceront l'abondance de la mer, et les choses les plus cachées dans le sable.
20 Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
Il dit aussi, touchant GAD: Béni soit celui qui fait élargir Gad; il habite comme un vieux lion, et il déchire bras et tête.
21 Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
Il a regardé le commencement [du pays pour l'avoir] pour soi, parce que c'était là qu'était cachée la portion du Législateur, et il est venu avec les principaux du peuple; il a fait la justice de l'Eternel, et ses jugements avec Israël.
22 Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
Et il dit touchant DAN: Dan est un jeune lion, il sautera de Basan.
23 Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
Il dit aussi touchant NEPHTHALI: Nephthali rassasié de bienveillance, et rempli de la bénédiction de l'Eternel, possède l'Occident et le Midi.
24 Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
Il dit aussi touchant ASER: Aser sera béni en enfants; il sera agréable à ses frères; [et] même il trempera son pied dans l'huile.
25 Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
Tes verrous seront de fer et d'airain, et ta force durera autant que tes jours.
26 “Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
Ô Droiturier, il n'y a point de [Dieu] semblable au [Dieu] Fort, qui [vient] à ton aide, porté sur les cieux et sur les nuées en sa Majesté.
27 Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
C'est une retraite que le Dieu qui est de tout temps, et [d'être] sous les bras éternels; car il a chassé de devant toi tes ennemis, et il a dit: Extermine.
28 Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
Israël donc habitera seul sûrement, l'œil de Jacob sera vers un pays de froment et de vin, et ses cieux distilleront la rosée.
29 Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”
Ô que tu es heureux, Israël! Qui est le peuple semblable à toi, lequel ait été gardé par l'Eternel, le bouclier de ton secours, et l'épée par laquelle tu as été hautement élevé? tes ennemis seront humiliés, et tu fouleras de tes pieds leurs lieux les plus hauts.

< Maimaitawar Shari’a 33 >