< Maimaitawar Shari’a 32 >

1 Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
Dêem ouvidos, céus, e eu vou falar. Que a terra ouça as palavras da minha boca.
2 Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
Minha doutrina cairá como a chuva. Meu discurso se condensará como o orvalho, como a chuva nebulosa sobre a grama tenra, como os chuveiros sobre a erva.
3 Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
Pois vou proclamar o nome de Yahweh. Atribuir grandeza ao nosso Deus!
4 Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
The Rock: seu trabalho é perfeito, pois todos os seus caminhos são justos. Um Deus de fidelidade que não faz nada de errado, justo e correto é ele.
5 Sun aikata mugunta a gabansa; saboda abin kunyarsu, su ba’ya’yansa ba ne, amma wata muguwar tsara ce, karkatacciya.
Eles têm lidado com ele de forma corrupta. Eles não são seus filhos, por causa de seu defeito. Eles são uma geração perversa e tortuosa.
6 Haka za ku biya Ubangiji, Ya ku wawaye da kuma mutane marasa hikima? Shi ba Ubanku ba ne, Mahaliccinku, wanda ya yi ku, ya kuma siffanta ku?
É assim que você paga a Javé, pessoas tolas e insensatas? Ele não é seu pai que o comprou? Ele o fez e o estabeleceu.
7 Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
Lembre-se dos dias de antigamente. Considere os anos de muitas gerações. Pergunte a seu pai, e ele lhe mostrará; seus anciãos, e eles lhe dirão.
8 Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan’ya’yan Isra’ila maza.
Quando o Altíssimo deu às nações a sua herança, quando ele separou os filhos dos homens, ele estabeleceu os limites dos povos de acordo com o número de filhos de Israel.
9 Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
Pois a parte de Yahweh é seu povo. Jacob é a maior parte de sua herança.
10 A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
Ele o encontrou em uma terra desértica, na selva de uivar de lixo. Ele o cercou. Ele cuidava dele. Ele o manteve como a maçã de seu olho.
11 kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta tana rufe’ya’yanta, ta buɗe fikafikanta don tă kwashe su tă ɗauke su a kafaɗunta.
Como uma águia que agita seu ninho, que agita sobre suas crias, ele espalhou suas asas para o exterior, ele os levou, ele as carregou em suas penas.
12 Ubangiji kaɗai ya jagorance shi; babu wani baƙon gunkin da yake tare da shi.
Yahweh sozinho o conduziu. Não havia nenhum deus estrangeiro com ele.
13 Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse ya ciyar da shi da amfanin gona. Ya shayar da shi da zuma daga dutse, da kuma mai daga dutsen ƙanƙara,
Ele o fez cavalgar nos lugares altos da terra. Ele comeu o aumento do campo. Ele o fez sugar o mel da rocha, óleo da rocha frágil;
14 da kindirmo da madara daga shanu da tumaki da ƙibabbun tumaki da awaki, da zaɓaɓɓun ragunan Bashan da kuma ƙwayoyin alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi ja wur mai kumfa.
manteiga do rebanho, e leite do rebanho, com gordura de cordeiros, carneiros da raça de Bashan, e caprinos, com o mais fino do trigo. Do sangue da uva, você bebeu vinho.
15 Yeshurun ya yi ƙiba, ya yi kauri; cike da abinci, ya zama da nauyi, ya kuma zama sumul. Ya yashe Allahn da ya yi shi, ya ƙi Dutse Cetonsa.
But Jeshurun engordou e chutou. Você engordou. Você se tornou grosso. Você se tornou elegante. Depois abandonou Deus, que o fez, e rejeitou a rocha de sua salvação.
16 Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu, suka husata shi da gumakan banƙyamarsu.
Eles o levaram a ter ciúmes com deuses estranhos. Eles o provocaram à raiva com abominações.
17 Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba, ga allolin da ba su sani ba, ga allolin da aka shigo da su daga baya, allolin da kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
Eles se sacrificaram aos demônios, não a Deus, a deuses que eles não conheciam, a novos deuses que surgiram recentemente, o que seus pais não temiam.
18 Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku; kuka manta da Allahn da ya haife ku.
Do rochedo que se tornou seu pai, você está desatento, e esqueceram de Deus que lhes deu à luz.
19 Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin’ya’yansa maza da mata sun husata shi.
Yahweh viu e abominou, por causa da provocação de seus filhos e suas filhas.
20 Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su, in ga ƙarshensu; gama su muguwar tsara ce,’ya’ya ne marasa aminci.
Ele disse: “Vou esconder meu rosto deles”. Vou ver qual será o fim deles; pois eles são uma geração muito perversa, crianças nas quais não há fidelidade.
21 Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba, suka kuma husata ni da gumakansu na wofi. Zan sa su yi kishi ta wurin waɗanda ba mutane ba; zan sa su yi fushi ta wurin al’ummar da ba ta da sani.
Eles me levaram ao ciúme com aquilo que não é Deus. Eles me provocaram à raiva com suas vaidades. Vou levá-los à inveja com aqueles que não são um povo. Eu os provocarei à raiva com uma nação tola.
22 Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol h7585)
Pois um incêndio se acende em minha raiva, que arde até o mais baixo Sheol, devora a terra com seu aumento, e pega fogo aos alicerces das montanhas. (Sheol h7585)
23 “Zan tula masifu a kansu in kuma gama kibiyoyina a kansu.
“Eu vou amontoar males sobre eles. Vou gastar minhas setas neles.
24 Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu, zazzaɓi mai zafi da muguwar annoba; zan aika da haƙoran namun jeji a kansu, da dafin mesa masu ja da ciki.
They deve ser desperdiçado com a fome, e devorado com calor abrasador e amarga destruição. Enviarei os dentes dos animais sobre eles, com o veneno de víboras que deslizam no pó.
25 Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, a cikin gidajensu kuma tsoro zai mamaye su.’Yan maza da’yan mata za su hallaka, haka ma jarirai da maza masu furfura.
Fora da espada, a espada desce, e nas salas, terror tanto sobre o jovem como sobre a virgem, a criança lactante com o homem de cabelo grisalho.
26 Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin’yan adam.
Eu disse que os espalharia para longe. Eu faria cessar a memória deles entre os homens;
27 Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’”
se não fosse por temer a provocação do inimigo, para que seus adversários não julguem erroneamente, para que não digam: “Nossa mão está exaltada”; Yahweh não fez tudo isso”.
28 Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
Pois eles são uma nação sem conselho. Não há neles nenhum entendimento.
29 A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
Oh, que eles foram sábios, que eles entenderam isso, que eles considerariam seu último fim!
30 Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
Como se pode perseguir mil, e dois colocaram dez mil para voar, a menos que sua rocha os tivesse vendido, e Yahweh os tinha entregue?
31 Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
Pois sua rocha não é como nossa rocha, até mesmo nossos próprios inimigos cedem.
32 Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma.’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
Pois a videira deles é da videira de Sodoma, dos campos de Gomorra. Suas uvas são uvas venenosas. Seus aglomerados são amargos.
33 Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
Their o vinho é o veneno das serpentes, o veneno cruel das áspides.
34 “Ban jibge wannan a ma’ajiya na kuma yimƙe shi a taskokina ba?
“Isto não está guardado comigo, selado entre meus tesouros?
35 Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa. A cikin lokaci, ƙafarsu za tă yi santsi; ranar masifarsu ta yi kusa hallakarsu kuma tana gaggautawa a kansu.”
A vingança é minha, e a recompensa é minha, no momento em que seus pés deslizam, pois o dia de sua calamidade está próximo. A desgraça deles corre sobre eles”.
36 Ubangiji zai shari’anta mutanensa yă kuma ji tausayin bayinsa sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya ƙare babu kowa kuma da ya rage, bawa ko’yantacce.
Pois Yahweh julgará seu povo, e ter compaixão de seus servos, quando ele vê que o poder deles se foi, que não há ninguém restante, calado ou deixado em liberdade.
37 Zai ce, “To, ina allolinsu, dutsen da suka yi mafaka a ciki,
Ele dirá: “Onde estão seus deuses”, a pedra na qual eles se refugiaram,
38 allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka kuma sha ruwan inabin hadayunsu? Ku sa su tashi su taimake ku mana! Bari su ba ku mafaka!
que comiam a gordura de seus sacrifícios, e beberam o vinho de sua oferta de bebida? Deixe-os se levantar e ajudá-los! Deixe-os ser sua proteção.
39 “Ku duba yanzu cewa ni ne Shi! Ba wani allah in ban da ni. Nakan kashe in kuma rayar, nakan sa rauni in kuma warkar, ba wanda yake da iko yă cece wani daga hannuna.
“Veja agora que eu mesmo sou ele”. Não há nenhum deus comigo. Eu mato e eu ganho vida. Eu ferimento e eu saro. Não há ninguém que possa entregar da minha mão.
40 Na ɗaga hannu sama na kuma furta. Muddin ina raye har abada,
Pois levanto minha mão para o céu e declaro, como eu vivo para sempre,
41 sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya hannuna kuwa ya cafke shi don yin hukunci, zan ɗau fansa a kan abokan gābana in sāka wa waɗanda suke ƙina.
se eu afiar minha espada cintilante, minha mão o agarra no julgamento; Vingar-me-ei de meus adversários, e retribuirá àqueles que me odeiam.
42 Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, yayinda takobina yana cin nama, jinin kisassu da na kamammu, kawunan shugabannin abokan gāba.”
Vou embebedar minhas setas com sangue. Minha espada devorará a carne com o sangue dos mortos e dos cativos, da cabeça dos líderes do inimigo”.
43 Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa, gama zai rama ɗau fansar jinin bayinsa; zai ɗau fansa a kan abokan gābansa yă kuma yi kafara domin ƙasarsa da mutanensa.
Alegrem-se, nações, com seu povo, pois ele vingará o sangue de seus servos. Ele se vingará de seus adversários, e fará expiação por sua terra e por seu povo.
44 Sai Musa ya zo da Yoshuwa ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
Moisés veio e falou todas as palavras desta canção aos ouvidos do povo, ele e Josué, o filho de Freira.
45 Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
Moisés terminou de recitar todas estas palavras para todo Israel.
46 ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
Ele lhes disse: “Ponham seu coração em todas as palavras que eu lhes testifico hoje, as quais vocês mandarão seus filhos observar, todas as palavras desta lei”.
47 Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
Pois não é coisa vã para vocês, porque é a sua vida, e através dela prolongarão seus dias na terra, onde atravessam o Jordão para possuí-la”.
48 A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh falou a Moisés nesse mesmo dia, dizendo:
49 “Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
“Suba a esta montanha de Abarim, ao Monte Nebo, que está na terra de Moab, que fica do outro lado de Jericó; e veja a terra de Canaã, que eu dou aos filhos de Israel por uma possessão.
50 A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
Morra na montanha onde você sobe, e seja recolhido ao seu povo, como Arão seu irmão morreu no Monte Hor, e foi recolhido ao seu povo;
51 Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
porque você transgrediu contra mim entre os filhos de Israel nas águas do Meribah de Cades, no deserto de Zin; porque você não defendeu minha santidade entre os filhos de Israel.
52 Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”
Pois vereis a terra à distância; mas não entrareis ali na terra que eu dou aos filhos de Israel”.

< Maimaitawar Shari’a 32 >