< Yoshuwa 1 >

1 Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
Agora após a morte de Moisés, servo de Iavé, Iavé falou a Josué, filho de Freira, servo de Moisés, dizendo:
2 “Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
“Moisés, meu servo, está morto”. Agora, pois, levantai-vos, atravessai este Jordão, vós e todo este povo, para a terra que lhes estou dando, até mesmo aos filhos de Israel”.
3 Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
Eu vos dei cada lugar que a sola de vosso pé pisará, como eu disse a Moisés.
4 Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
Do deserto e deste Líbano até o grande rio, o rio Eufrates, toda a terra dos hititas, e até o grande mar em direção ao pôr do sol, será sua fronteira.
5 Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
Nenhum homem será capaz de estar diante de você todos os dias de sua vida. Como eu estive com Moisés, assim eu estarei com vocês. Não vos falharei nem vos abandonarei.
6 “Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
“Seja forte e corajoso; pois você fará com que este povo herde a terra que jurei a seus pais lhes dar.
7 Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
“Sejam fortes e muito corajosos. Tende o cuidado de observar para fazer de acordo com toda a lei que Moisés, meu servo, vos ordenou. Não se desvie dela para a mão direita ou para a esquerda, para que possa ter bom êxito onde quer que vá.
8 Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
Este livro da lei não sairá de sua boca, mas meditará nele dia e noite, para que você possa observar para fazer de acordo com tudo o que nele está escrito; pois então você fará seu caminho prosperar, e então você terá bom êxito.
9 Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
Eu não te ordenei? Seja forte e corajoso. Não tenha medo. Não se assuste, pois Yahweh seu Deus está com você onde quer que você vá”.
10 Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
Então Josué comandou os oficiais do povo, dizendo:
11 “Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
“Passem pelo meio do acampamento e comandem o povo, dizendo: 'Preparem comida; porque dentro de três dias vocês devem passar por este Jordão, para entrar para possuir a terra que Yahweh vosso Deus vos dá para possuir'”.
12 Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
Josué falou aos rubenitas, e aos gaditas, e à meia tribo de Manassés, dizendo:
13 “Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
“Lembrai-vos da palavra que Moisés, servo de Javé, vos ordenou, dizendo: 'Javé, vosso Deus, vos dá descanso, e vos dará esta terra.
14 Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
Vossas esposas, vossos pequenos e vosso gado viverão na terra que Moisés vos deu além do Jordão; mas vós passareis diante de vossos irmãos armados, todos os homens valentes, e os ajudareis
15 har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
até que Javé tenha dado descanso a vossos irmãos, como ele vos deu, e eles também possuíram a terra que Javé vosso Deus lhes dá. Então retornareis à terra de vossa posse e a possuireis, que Moisés, servo de Javé, vos deu além do Jordão, em direção ao nascer do sol”.
16 Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
Eles responderam a Joshua, dizendo: “Tudo o que você nos ordenou, faremos e para onde quer que você nos envie, iremos”.
17 Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
Assim como ouvimos Moisés em todas as coisas, também nós o ouviremos a você”. Somente Yahweh, seu Deus, possa estar com você, como estava com Moisés.
18 Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”
Quem se rebelar contra seu mandamento e não escutar suas palavras em tudo o que você lhe ordenar, será ele mesmo condenado à morte. Sede apenas fortes e corajosos”.

< Yoshuwa 1 >