< Daniyel 5 >

1 Sarki Belshazar ya yi babban biki domin dubban hakimansa ya kuma sha ruwan inabi tare da su.
Balsazar král učinil hody veliké tisíci knížatům svým, a před nimi víno pil.
2 Yayinda Belshazar yake shan ruwan inabi, sai ya umarta a kawo zinariya da azurfan da Nebukadnezzar mahaifinsa ya kwaso daga haikali a Urushalima, saboda sarki da hakimansa, da matansa da ƙwarƙwaransa su sha da su.
A když pil víno Balsazar, rozkázal přinésti nádobí zlaté a stříbrné, kteréž vynesl Nabuchodonozor otec jeho z chrámu Jeruzalémského, aby z něho pili král i knížata jeho, ženy jeho i ženiny jeho.
3 Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
I přineseno jest nádobí zlaté, kteréž vynesli z chrámu domu Božího, kterýž byl v Jeruzalémě, a pili z něho král i knížata jeho, ženy jeho i ženiny jeho.
4 Yayinda suke shan ruwan inabin, sai suka yabi allolin zinariya da azurfa, da na tagulla, da na ƙarfe, da na itace da kuma na dutse.
Pili víno, a chválili bohy zlaté a stříbrné, měděné, železné, dřevěné a kamenné.
5 Nan da nan sai ga yatsotsin hannun mutum sun bayyana, suna yin rubutu a kan shafen bangon, kusa da wurin da ake ajiye fitilar fadar sarki. Sarki kuwa yana ganin hannun yayinda yake rubutu.
V touž hodinu vyšli prstové ruky lidské, a psali naproti svícnu na stěně paláce královského, a král hleděl na částky ruky, kteráž psala.
6 Sai fuskarsa ta ruɗe, ya kuma ji tsoro ƙwarai har gwiwoyinsa suka yi ta bugun juna, ƙafafunsa kuma suka rasa ƙarfi.
Tedy jasnost královská změnila se, a myšlení jeho zkormoutila ho, a pasové bedr jeho rozpásali se, i kolena jeho jedno o druhé se tlouklo.
7 Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
A zkřikl král ze vší síly, aby přivedeni byli hvězdáři, Kaldejští a hadači. I mluvil král a řekl mudrcům Babylonským: Kdokoli přečte psání toto, a výklad jeho mi oznámí, šarlatem odín bude, a řetěz zlatý na hrdlo jeho, a třetím v království po mně bude.
8 Sa’an nan sai dukan masu hikima suka zo ciki, amma ba su iya karanta rubutun ba ko su faɗa wa sarki abin da yake nufi.
I předstoupili všickni mudrci královští, ale nemohli písma toho čísti, ani výkladu oznámiti králi.
9 Saboda haka Sarki Belshazar ya firgita ƙwarai kuma fuskarsa ta ƙara ruɗewa. Hakimansa kuma suka rikice.
Pročež král Balsazar velmi předěšen byl, a jasnost jeho změnila se na něm, ano i knížata jeho zkormouceni byli.
10 Sai sarauniya, da jin muryoyi na sarki da na hakimansa, ta shiga babban ɗakin liyafar. Ta ce, “Ya sarki, ranka yă daɗe! Kada ka firgita! Kada fuskarka ta ruɗe!
Královna pak, příčinou té věci královské a knížat jeho, do domu těch hodů vešla, a promluvivši královna, řekla: Králi, na věky živ buď. Nechť tě neděsí myšlení tvá, a jasnost tvá nechť se nemění.
11 Akwai wani mutum a masarautarka wanda yake da ruhun alloli masu tsarki a cikinsa. A zamanin mahaifinka an gane cewa yana da basira da hazaka da hikima kamar na alloli. Sarki Nebukadnezzar mahaifinka, mahaifinka sarki, na ce, ya naɗa shugaban masu dabo, da masu sihiri, masanan taurari da kuma masu duba.
Jest muž v království tvém, v němž jest duch bohů svatých, v kterémž za dnů otce tvého osvícení, rozumnost a moudrost, jako moudrost bohů, nalezena, jehož král Nabuchodonozor otec tvůj knížetem mudrců, hvězdářů, Kaldejských a hadačů ustanovil, otec tvůj, ó králi,
12 Wannan mutum Daniyel, wanda sarki ya kira Belteshazar, an gane yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma’anar kacici-kacici, da warware al’amura masu wuya. Ka kira Daniyel shi kuwa zai faɗa maka abin da rubutun nan yake nufi.”
Proto že duch znamenitý, i umění a rozumnost vykládání snů a oznámení pohádek, i rozvázání věcí nesnadných nalezeno při Danielovi, jemuž král jméno dal Baltazar. Nechať nyní zavolán jest Daniel, a oznámíť výklad ten.
13 Saboda haka aka kawo Daniyel a gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda mahaifina sarki ya kawo daga Yahuda?
Tedy přiveden jest Daniel před krále. I mluvil král a řekl Danielovi: Ty-li jsi ten Daniel, jeden z synů zajatých Judských, kteréhož přivedl král otec můj z Judstva?
14 Na sami labari cewa kana da ruhun alloli a cikinka da kuma basira, da hazaka da kuma fitacciyar hikima.
Slyšel jsem zajisté o tobě, že duch bohů svatých jest v tobě, a osvícení i rozumnost a moudrost znamenitá nalezena jest v tobě.
15 An kawo masu hikima da masu dabo a gabana domin su karanta wannan rubutu su kuma faɗa mini abin da yake nufi, amma ba su iya ba.
A nyní přivedeni jsou přede mne mudrci a hvězdáři, aby mi písmo toto přečtli, a výklad jeho oznámili, a však nemohli výkladu věci té oznámiti.
16 Na sami labari cewa kana iya ba da fassara da kuma warware matsaloli masu wuya. In har ka iya karanta wannan rubutun ka kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
Já pak slyšel jsem o tobě, že můžeš to, což jest nesrozumitelného, vykládati, a což nesnadného, rozvázati. Protož nyní, budeš-li moci písmo to přečísti, a výklad jeho mně oznámiti, v šarlat oblečen budeš, a řetěz zlatý na hrdlo tvé, a třetím v království po mně budeš.
17 Sai Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, “Za ka iya ajiye kyautar wa kanka ko kuma ka ba wa wani. Duk da haka, zan karanta wa sarki rubutun, in kuma faɗa abin da yake nufi.
Tedy odpověděl Daniel a řekl před králem: Darové tvoji nechť zůstávají tobě, a odplatu svou dej jinému, a však písmo přečtu králi, a výklad oznámím jemu.
18 “Ya sarki, Allah Mafi Ɗaukaka ya ba mahaifinka Nebukadnezzar sarauta, da girma, da ɗaukaka, da martaba.
Ty králi, slyš: Bůh nejvyšší královstvím a důstojností i slávou a okrasou obdařil Nabuchodonozora otce tvého,
19 Saboda irin matsayin da ya ba shi, dukan mutane da al’ummai da kuma dukan harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani.
A pro důstojnost, kterouž ho obdařil, všickni lidé, národové a jazykové třásli a báli se před ním. Kohokoli chtěl, zabil, a kterékoli chtěl, bil, kteréž chtěl, povyšoval, a kteréž chtěl, ponižoval.
20 Amma da lokacin da zuciyarsa ta cika da girman kai ta kuma taurare, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.
Když se pak bylo pozdvihlo srdce jeho, a duch jeho zmocnil se v pýše, ssazen byl z stolice království svého, a slávu odjali od něho.
21 Aka kore shi daga cikin mutane aka kuma ba shi tunani irin na dabba; ya yi zama tare da jakunan jeji, ya kuma ci ciyawa kamar shanu; jikinsa kuma ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
Ano i z spolku synů lidských vyvržen byl, a srdce jeho zvířecímu podobné učiněno bylo, a s divokými osly bylo bydlení jeho. Bylinu jako volům dávali jemu jísti, a rosou nebeskou tělo jeho smáčíno bylo, dokudž nepoznal, že panuje Bůh nejvyšší nad královstvím lidským, a že kohož chce, ustanovuje nad ním.
22 “Amma kai ɗansa, Ya Belshazar, ba ka ƙasƙantar da kanka ba, ko da yake ka san wannan duka.
Ty také, synu jeho Balsazaře, neponížil jsi srdce svého, ačkolis o tom o všem věděl.
23 A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
Ale pozdvihls se proti Pánu nebes; nebo nádobí domu jeho přinesli před tebe, a ty i knížata tvá, ženy tvé i ženiny tvé pili jste víno z něho. Nadto bohy stříbrné a zlaté, měděné, železné, dřevěné a kamenné, kteříž nevidí, ani slyší, aniž co vědí, chválil jsi, Boha pak, v jehož ruce jest dýchání tvé i všecky cesty tvé, neoslavoval jsi.
24 Saboda haka ya aiko da hannun da ya yi rubutun nan.
Protož nyní od něho poslána jest částka ruky této, a písmo to napsáno jest.
25 “Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
A totoť jest písmo napsané: Mene, mene, tekel, ufarsin, totiž: Zčetl jsem, zčetl, zvážil a rozděluji.
26 “Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
Tento pak jest výklad slov: Mene, zčetl Bůh království tvé, a k konci je přivedl.
27 “Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
Tekel, zvážen jsi na váze, a nalezen jsi lehký.
28 “Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
Peres, rozděleno jest království tvé, a dáno jest Médským a Perským.
29 Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
Tedy z rozkazu Balsazarova oblékli Daniele v šarlat, a řetěz zlatý dali na hrdlo jeho, a rozhlašovali o něm, že má býti pánem třetím v království.
30 A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
V touž noc zabit jest Balsazar král Kaldejský.
31 Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.
Darius pak Médský ujal království v letech okolo šedesáti a dvou.

< Daniyel 5 >