< Daniyel 11 >

1 A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
A tak já léta prvního Daria Médského postavil jsem se, abych ho zmocňoval a posiloval.
2 “Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
Již pak oznámímť pravdu: Aj, ještě tři králové kralovati budou v Perské zemi; potom čtvrtý zbohatne bohatstvím velikým nade všecky, a když se zmocní v bohatství svém, vzbudí všecky proti království Řeckému.
3 Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
I povstane král mocný, kterýž bude míti panství široké, a bude činiti podlé vůle své.
4 Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
Když se pak zmocní, potříno bude království jeho, a rozděleno bude na čtyři strany světa, však ne mezi potomky jeho, aniž bude panství jeho takové, jakéž bylo; nebo vykořeněno bude království jeho, a jiným mimo ně se dostane.
5 “Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
Pročež posilní se král polední, ano i jedno z knížat jeho, a mocnější bude nad něho, a panovati bude; panství široké bude panství jeho.
6 Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
Po některých pak letech spřízní se; nebo dcera krále poledního dostane se za krále půlnočního, aby učinila příměří. Ale neobdrží síly ramene, aniž on ostojí s ramenem svým, ale vydána bude ona i ti, kteříž ji přivedou, i syn její, i ten, kterýž ji posilňoval v ty časy.
7 “Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
Potom povstane z výstřelku kořenů jejích na místo jeho, kterýž přitáhne s vojskem svým, a udeří na pevnost krále půlnočního, a přičiní se, aby se jich zmocnil.
8 Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
Nadto i bohy jejich s knížaty jejich, s nádobami drahými jejich, stříbrem a zlatem v zajetí zavede do Egypta, a bude bezpečen za mnoho let před králem půlnočním.
9 Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
A tak přijde do království král polední, a navrátí se do země své.
10 ’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
Ale synové onoho válčiti budou, a seberou množství vojsk velikých. A nenadále přijda, jako povodeň procházeti bude, a navracuje se, válkou dotírati bude až k jeho pevnostem.
11 “Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
Pročež rozdrážděn jsa král polední, vytáhne, a bojovati bude s ním, s králem půlnočním, a sšikuje množství veliké, i bude vydáno množství to v ruku jeho.
12 Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
I pozdvihne se množství to, a povýší se srdce jeho, a ačkoli porazí na tisíce, a však se nezmocní.
13 Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
Potom navrátě se král půlnoční, sšikuje množství větší než prvé, a po dokonání času některých let, nenadále přijde s vojskem velikým a s dostatkem hojným.
14 “A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
V těch časích mnozí se postaví proti králi polednímu, ale synové nešlechetní z lidu tvého zhubeni budou, a pro stvrzení vidění tohoto padnou.
15 Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
Nebo přitáhne král půlnoční, a vzdělaje náspy, dobude měst hrazených, tak že ramena poledního neostojí, ani lid vybraný jeho, aniž budou míti síly k odpírání.
16 Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
A přitáhna proti němu, bude činiti podlé vůle své, a nebude žádného, ješto by se postavil proti němu. Postaví se také v zemi Judské, kterouž docela zkazí rukou svou.
17 Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
Potom obrátí tvář svou, aby přitáhna s mocí všeho království svého, a ukazuje se jako by vše upřímě jednal, dovede něčeho. Nebo dá jemu krásnou pannu, aby ho zahubil skrze ni, ale ona nedostojí aniž bude držeti s ním.
18 Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
Zatím obrátí tvář svou k ostrovům, a dobude mnohých, ale vůdce přítrž učiní pohanění jeho, anobrž to hanění jeho na něj obrátí.
19 Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
Pročež obrátí tvář svou k pevnostem země své, ale klesne a padne, i zahyne.
20 “Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
I povstane na místo jeho v slávě královské ten, kterýž rozešle výběrčí, ale ten po nemnohých dnech potřín bude, a to ne v hněvě, ani v boji.
21 “Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
Na místě tohoto postaví se nevzácný, ačkoli nevloží na něj ozdoby královské, a však přijda pokojně, ujme království skrze úlisnost.
22 Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
A rameny jako povodní zachváceni budou před oblíčejem jeho mnozí, a potříni budou jako i ten vůdce, kterýž s ním smlouvu učinil.
23 Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
Nebo v tovaryšství s ním vejda, prokáže nad ním lest, a přijeda, zmocní se království s malým počtem lidu.
24 Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
Bezpečně také i do nejúrodnějších míst té krajiny vpadne, a činiti bude to, čehož nečinili otcové jeho, ani otcové otců jeho; loupež a kořisti a zboží jim rozdělí, ano i proti pevnostem chytrosti své vymýšleti bude, a to do času.
25 “Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
Potom vzbudí sílu svou a srdce své proti králi polednímu s vojskem velikým, s nímž král polední vojensky se potýkati bude, s vojskem velikým a velmi silným, ale neostojí, proto že vymyslí proti němu chytrost.
26 Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
Nebo kteříž jídají pokrm, potrou jej, když vojsko onoho se rozvodní; i padnou, zbiti jsouce mnozí.
27 Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
Tehdáž obou těch králů srdce bude činiti zlé, a za jedním a týmž stolem lež mluviti budou, ale nepodaří se, proto že cíl uložený na jiný ještě čas odložen.
28 “Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
A protož navrátí se do země své s zbožím velikým, a srdce jeho bude proti smlouvě svaté. Což učině, navrátí se do země své.
29 “A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
V uložený čas navrátě se, potáhne na poledne, ale to nebude podobné prvnímu ani poslednímu.
30 Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
Nebo přijdou proti němu lodí Citejské, pročež bude jej to boleti, tak že opět zlobiti se bude proti smlouvě svaté. Což učině, navrátí se, a srozumění míti bude s těmi, kteříž opustili smlouvu svatou.
31 “Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
A vojska veliká podlé něho státi budou, a poškvrní svatyně a pevnosti; odejmou také obět ustavičnou, a postaví ohavnost zpuštění,
32 Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
Tak aby ty, kteříž se bezbožně proti smlouvě chovati budou, v pokrytství posiloval úlisnostmi, lid pak, kterýž zná Boha svého, aby jímali. Což i učiní.
33 “Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
Pročež vyučující lid, vyučující mnohé, padati budou od meče a ohně, zajetí a loupeže za mnohé dny.
34 Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
A když padati budou, malou pomoc míti budou; nebo připojí se k nim mnozí pochlebně.
35 Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
Z těch pak, kteříž jiné vyučují, padati budou, aby prubováni a čištěni a bíleni byli až do času jistého; neboť to ještě potrvá až do času uloženého.
36 “Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
Král zajisté ten bude činiti podlé vůle své, a pozdvihne se a zvelebí nad každého boha, i proti Bohu nade všemi bohy nejsilnějšímu mluviti bude divné věci; a šťastně se mu povede až do vykonání prchlivosti, ažby se to, což uloženo jest, vykonalo.
37 Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
Ani k bohům otců svých se nenakloní, ani k milování žen, aniž k komu z bohů se nakloní, proto že se nade všecko velebiti bude.
38 A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
A na místě Boha nejsilnějšího ctíti bude boha, kteréhož neznali otcové jeho; ctíti bude zlatem a stříbrem, a kamením drahým a klénoty.
39 Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
A tak dovede toho, že pevnosti Nejsilnějšího budou boha cizího, a kteréž se mu viděti bude, poctí slávou, a způsobí, aby panovali nad mnohými, a zemi rozdělí místo mzdy.
40 “A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
Při dokonání pak toho času trkati se s ním bude král polední, ale král půlnoční oboří se na něj s vozy a s jezdci a lodími mnohými, a přitáhna do zemí, jako povodeň projde.
41 Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
Potom přitáhne do země Judské, a mnohé země padnou. Tito pak ujdou ruky jeho, Idumejští a Moábští, a prvotiny synů Ammon.
42 Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
A když ruku svou vztáhne na země, ani země Egyptská nebude moci jeho zniknouti.
43 Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
Nebo opanuje poklady zlata a stříbra, a všecky klénoty Egyptské; Lubimští také a Mouřenínové za ním půjdou.
44 Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
V tom noviny od východu a od půlnoci přestraší jej; pročež vytáhne s prchlivostí velikou, aby hubil a mordoval mnohé.
45 Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.
I rozbije stany paláce svého mezi mořemi, na hoře okrasy svatosti; a když přijde k skonání svému, nebude míti žádného spomocníka.

< Daniyel 11 >