< Amos 2 >

1 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
Voici ce que dit le Seigneur: Ce n'est point à cause des triples et quadruples impiétés de Moab que Je le prendrai en aversion, c'est parce qu'il a brûlé les os du roi de l'Idumée, jusqu'à les réduire en poudre.
2 Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
Et Je lancerai la flamme sur Moab; et elle dévorera les fondations de ses villes, et Moab périra dans l'impuissance, au milieu des cris et au son des trompettes.
3 Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
Et Je détruira son juge, et J'exterminerai ses princes avec lui, dit le Seigneur.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
Voici ce que dit le Seigneur: Ce n'est point à cause des triples et quadruples impiétés des fils de Juda que Je les prendrai en aversion, c'est parce qu'ils ont répudié la loi du Seigneur, et qu'ils n'ont point gardé les commandements, et que les vaines idoles qu'ils avaient fabriquées et qu'avaient suivies leurs pères les ont eux-mêmes égarés.
5 Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
Et Je lancerai la flamme sur Juda, et elle dévorera les fondations de Jérusalem.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
Voici ce que dit le Seigneur: Ce n'est point à cause des triples et quadruples impiétés d'Israël que Je le prendrai en aversion; c'est parce qu'il a livré le juste à prix d'argent, et le pauvre pour des sandales
7 Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
que l'on traîne dans la poussière des chemins; c'est parce qu'ils ont frappé du poing la tête de l'indigent, qu'ils ont fait dévier le faible, et que le fils et le père ont eu la même concubine, afin de profaner le Nom de leur Dieu,
8 Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
et parce que, liant avec des cordes leurs manteaux, ils en ont voilé l'autel, et bu le vin des calomnies, dans le temple de leur Dieu.
9 “Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
Cependant c'est Moi qui ai, devant leur face, chassé l'Amorrhéen d'où il était; sa taille était celle du cèdre, sa force celle du chêne; et J'ai desséché ses fruits au-dessus de la terre, et ses racines au-dessous.
10 Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
Et vous, Je vous ai ramenés de la terre d'Égypte, et Je vous ai conduits çà et là dans le désert, pendant quarante ans, pour vous donner ensuite en héritage la terre des Amorrhéens.
11 “Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
Et J'ai pris de vos fils pour en faire des prophètes, et de vos jeunes enfants pour Me les consacrer; tout cela n'est-il pas vrai, fils d'Israël? dit le Seigneur.
12 “Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
Et vous faites boire du vin aux Nazaréens, et vous donnez des ordres aux prophètes, disant: Ne prophétisez pas!
13 “Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
Et, à cause de cela, voilà que Je vais rouler sur vous, comme un chariot rempli de paille.
14 Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
Et il n'y aura pas de fuite pour le coureur, et le fort ne pourra se prévaloir de sa force, et le guerrier ne sauvera pas sa vie;
15 ’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
et l'archer ne résistera pas, et l'homme aux pieds légers ne saura s'échapper, et le cavalier ne sauvera pas sa vie.
16 Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.
Et le fort ne mettra plus son cœur en ses forces; et, nu, il s'enfuira en ce jour, dit le Seigneur.

< Amos 2 >