< Yowel 3 >

1 “A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
Car voici qu'en ce temps, et en ces jours-là, quand J'aurai fait revenir de la captivité Juda et Jérusalem,
2 zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
J'assemblerai toutes les nations et les conduirai dans la vallée de Josaphat; là Je plaiderai avec elles pour Mon peuple et pour Israël, Mon héritage: car elles l'ont dispersé parmi les Gentils, qui se sont partagé Ma terre.
3 Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
Et ils ont tiré Mon peuple au sort, et ils ont livré des enfants à la prostitution, et ils ont vendu des jeunes filles pour du vin, et ils ont bu.
4 “Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
Or, qu'y a-t-il entre vous et Moi, Tyr, Sidon, Galilée des Philistins? Est-ce que vous pourrez user de représailles avec Moi? Ou Me garderez-vous rancune en votre cœur? Je vous rétribuerai, Moi, vite et sévèrement, sur vos têtes:
5 Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
Parce que vous avez pris Mon argent et Mon or; parce que vous avez porté dans vos temples Mes ornements précieux;
6 Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
parce que vous avez vendu aux fils des Grecs les fils de Juda et les fils de Jérusalem, pour les chasser de leurs frontières.
7 “Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
Mais voilà que Je les ramènerai des contrées où vous les avez conduits, et Je vous rétribuerai sur vos têtes.
8 Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
Et Je donnerai vos fils et vos filles aux fils de Juda, pour qu'ils les vendent comme captifs chez une nation lointaine; ainsi a parlé le Seigneur.
9 Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
Publiez ces choses parmi les Gentils; sanctifiez la guerre; excitez les combattants, vous tous hommes exercés aux armes; rassemblez-vous, et partez.
10 Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
Forgez des glaives avec vos socs de charrue, et, avec vos faux, des javelines. Que le faible lui-même dise: Je suis fort.
11 Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
Venez tous ensemble et entrez, vous nations d'alentour; vous, fils d'Israël, réunissez-vous là: que l'homme pacifique devienne un guerrier.
12 “Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
Que toutes les nations se lèvent; qu'elles se rendent dans la vallée de Josaphat; c'est là que Je siège pour juger les nations d'alentour.
13 Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
Envoyez des faucilles, car le vendangeur est prêt; entrez et foulez aux pieds les grappes, car le pressoir est plein; laissez déborder les cuves, car leur méchanceté a comble la mesure.
14 Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
Les échos ont retenti dans la vallée du jugement; car le jour du Seigneur est proche dans la vallée du jugement.
15 Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
Le soleil et la terre seront enveloppés de ténèbres, et les étoiles retireront leur lumière.
16 Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
Le Seigneur jettera de grands cris du haut de Sion; Il fera entendre Sa voix du haut de Jérusalem; le ciel et la terre trembleront; mais le Seigneur épargnera Son peuple, et Il fortifiera les fils d'Israël.
17 “Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
Et vous connaîtrez que Je suis le Seigneur votre Dieu, qui réside en Sion, sur la montagne sainte; et Jérusalem sera sainte, et les étrangers n'y passeront plus.
18 “A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
Et il arrivera qu'en ce jour-là les montagnes ruisselleront de douceur, et les collines de lait; et l'eau coulera de toutes les sources de Juda, et une fontaine jaillira de la maison du Seigneur, et elle abreuvera le val de Sétim.
19 Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
L'Égypte sera mise à néant; l'Idumée sera un champ de désolation, à cause des iniquités de ses fils contre Juda, parce qu'ils ont versé le sang innocent sur leur terre.
20 Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
Et la Judée sera habitée dans tous les siècles, et Jérusalem dans les générations des générations.
21 Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”
Et Je rechercherai leur sang, et Je n'absoudrai point ceux qui l'ont versé, et le Seigneur aura Son tabernacle en Sion.

< Yowel 3 >