< Ayyukan Manzanni 8 >

1 Shawulu kuwa yana can, yana tabbatar da mutuwarsa. A wannan rana wani babban tsanani ya auka wa ikkilisiyar da take a Urushalima, sai duka suka warwatsu ko’ina a Yahudiya da Samariya, manzanni kaɗai ne suka rage.
And Saul was consenting to his death. And at that time there was raised a great persecution against the church which was at Jerusalem; and they were all dispersed through the countries of Judea, and Samaria, except the apostles.
2 Mutane masu tsoron Allah suka binne Istifanus suka kuma yi makoki ƙwarai dominsa.
And devout men took order for Stephen’s funeral, and made great mourning over him.
3 Amma Shawulu ya fara hallaka ikkilisiya. Yana shiga gida-gida, yana jan maza da mata yana jefa su cikin kurkuku.
But Saul made havock of the church, entering in from house to house, and dragging away men and women, committed them to prison.
4 Waɗanda aka wartsar suka yi ta wa’azin maganar a duk inda suka tafi.
They therefore that were dispersed, went about preaching the word of God.
5 Filibus ya gangara zuwa wani birni a Samariya ya kuma yi shelar Kiristi a can.
And Philip going down to the city of Samaria, preached Christ unto them.
6 Sa’ad da taron mutane suka ji Filibus suka kuma ga abubuwan banmamakin da ya yi, sai duk suka mai da hankali sosai ga abin da ya faɗa.
And the people with one accord were attentive to those things which were said by Philip, hearing, and seeing the miracles which he did.
7 Mugayen ruhohi suka fiffito suna kururuwa daga cikin mutane da yawa, shanyayyu da guragu masu yawa suka sami warkarwa.
For many of them who had unclean spirits, crying with a loud voice, went out.
8 Saboda haka aka yi farin ciki ƙwarai a birnin.
And many, taken with the palsy, and that were lame, were healed.
9 To, akwai wani mutum mai suna Siman wanda ya kwana biyu yana yin sihiri a birnin har ya ba wa duk mutanen Samariya mamaki. Ya kuma yi taƙama cewa shi wani mai girma ne,
There was therefore great joy in that city. Now there was a certain man named Simon, who before had been a magician in that city, seducing the people of Samaria, giving out that he was some great one:
10 dukan mutane kuwa, manyan da ƙanana, suka mai da hankali gare shi suka kuma ce, “Mutumin nan shi ne ikon Allah da aka sani a matsayin Iko Mai Girma”
To whom they all gave ear, from the least to the greatest, saying: This man is the power of God, which is called great.
11 Suka bi shi domin ya daɗe yana ba su mamaki da sihirinsa.
And they were attentive to him, because, for a long time, he had bewitched them with his magical practices.
12 Amma da suka gaskata da Filibus sa’ad da yake wa’azin labari mai daɗi na mulkin Allah da kuma sunan Yesu Kiristi, sai aka yi musu baftisma, maza da mata.
But when they had believed Philip preaching of the kingdom of God, in the name of Jesus Christ, they were baptized, both men and women.
13 Siman kansa ya gaskata aka kuma yi masa baftisma. Ya kuma bi Filibus ko’ina, yana mamakin manyan alamu da ayyukan banmamakin da ya gani.
Then Simon himself believed also; and being baptized, he adhered to Philip. And being astonished, wondered to see the signs and exceeding great miracles which were done.
14 Sa’ad da manzannin da suke a Urushalima suka ji cewa Samariya ta karɓi maganar Allah, sai suka aika musu da Bitrus da Yohanna.
Now when the apostles, who were in Jerusalem, had heard that Samaria had received the word of God, they sent unto them Peter and John.
15 Da suka iso, sai suka yi musu addu’a domin su karɓi Ruhu Mai Tsarki,
Who, when they were come, prayed for them, that they might receive the Holy Ghost.
16 domin Ruhu Mai Tsarki bai riga ya sauka wa waninsu ba tukuna, an dai yi musu baftisma ne kawai a cikin sunan Ubangiji Yesu.
For he was not as yet come upon any of them; but they were only baptized in the name of the Lord Jesus.
17 Sa’an nan Bitrus da Yohanna suka ɗibiya hannuwansu a kansu, suka kuwa karɓi Ruhu Mai Tsarki.
Then they laid their hands upon them, and they received the Holy Ghost.
18 Sa’ad da Siman ya ga cewa ana ba da Ruhu ta wurin ɗibiya hannuwan manzannin, sai ya miƙa musu kuɗi,
And when Simon saw, that by the imposition of the hands of the apostles, the Holy Ghost was given, he offered them money,
19 ya ce, “Ni ma ku ba ni wannan iyawa don kowa na ɗibiya wa hannuwana yă karɓi Ruhu Mai Tsarki.”
Saying: Give me also this power, that on whomsoever I shall lay my hands, he may receive the Holy Ghost. But Peter said to him:
20 Bitrus ya amsa ya ce, “Bari kuɗinka ya hallaka tare da kai, domin ka yi tsammani za ka iya saya kyautar Allah da kuɗi!
Keep thy money to thyself, to perish with thee, because thou hast thought that the gift of God may be purchased with money.
21 Ba ruwanka da wannan hidimar, domin zuciyarka ba daidai take a gaban Allah ba.
Thou hast no part nor lot in this matter. For thy heart is not right in the sight of God.
22 Ka tuba daga wannan mugunta ka kuma yi addu’a ga Ubangiji. Wataƙila zai gafarta maka don irin tunanin da yake a zuciyarka.
Do penance therefore for this thy wickedness; and pray to God, that perhaps this thought of thy heart may be forgiven thee.
23 Gama na lura kana cike da ɗacin rai kana kuma daure cikin zunubi.”
For I see thou art in the gall of bitterness, and in the bonds of iniquity.
24 Sai Siman ya amsa ya ce, “Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda ni don kada ko ɗaya daga cikin abin da ka faɗa ya same ni.”
Then Simon answering, said: Pray you for me to the Lord, that none of these things which you have spoken may come upon me.
25 Sa’ad da suka yi shaidar suka kuma yi shelar maganar Ubangiji, sai Bitrus da Yohanna suka koma Urushalima, suna wa’azin bishara a ƙauyukan Samariya masu yawa.
And they indeed having testified and preached the word of the Lord, returned to Jerusalem, and preached the gospel to many countries of the Samaritans.
26 To wani mala’ikan Ubangiji ya ce wa Filibus, “Ka yi kudu zuwa hanyar, hanyar hamada, da ta gangara daga Urushalima zuwa Gaza.”
Now an angel of the Lord spoke to Philip, saying: Arise, go towards the south, to the way that goeth down from Jerusalem into Gaza: this is desert.
27 Saboda haka ya kama hanya, a kan hanyarsa kuwa sai ya sadu da wani mutumin Itiyofiya, wanda yake bābā, hafsa mai muhimmanci wanda yake lura da dukan ma’ajin Kandas (wanda yake nufin “sarauniyar mutanen Itiyofiya”). Mutumin nan ya tafi Urushalima ne domin yin sujada,
And rising up, he went. And behold a man of Ethiopia, an eunuch, of great authority under Candace the queen of the Ethiopians, who had charge over all her treasures, had come to Jerusalem to adore.
28 a kan hanyarsa ta komawa gida kuwa yana zaune bisan keken yaƙinsa yana karatun littafin annabin Ishaya.
And he was returning, sitting in this chariot, and reading Isaias the prophet.
29 Sai Ruhu ya ce wa Filibus, “Matsa wurin kekunan yaƙin nan ka yi kusa da ita.”
And the Spirit said to Philip: Go near, and join thyself to this chariot.
30 Sai Filibus ya ruga zuwa wajen keken yaƙin ya kuma ji mutumin yana karatun littafin annabin Ishaya. Filibus ya yi tambaya ya ce, “Ka fahimci abin da kake karantawa?”
And Philip running thither, heard him reading the prophet Isaias. And he said: Thinkest thou that thou understandest what thou readest?
31 Sai ya ce, “Ina fa zan iya, in ba dai wani ya fassara mini ba?” Saboda haka sai ya gayyaci Filibus yă hau yă zauna tare da shi.
Who said: And how can I, unless some man shew me? And he desired Philip that he would come up and sit with him.
32 Bābān yana karanta wannan Nassin, “An ja shi kamar tunkiya zuwa mayanka, kuma kamar ɗan rago a hannun mai askin gashinsa yake shiru, haka kuwa bai buɗe bakinsa ba.
And the place of the scripture which he was reading was this: He was led as a sheep to the slaughter; and like a lamb without voice before his shearer, so openeth he not his mouth.
33 A cikin wulaƙacinsa aka hana masa gaskiya. Wa zai iya yin zancen zuriyarsa? Gama an ɗauke ransa daga duniya.”
In humility his judgment was taken away. His generation who shall declare, for his life shall be taken from the earth?
34 Sai bābān ya tambayi Filibus ya ce, “Ka gaya mini, ina roƙonka, annabin yana magana a kan wane ne, kansa ne, ko kuwa wani dabam?”
And the eunuch answering Philip, said: I beseech thee, of whom doth the prophet speak this? of himself, or of some other man?
35 Sa’an nan Filibus ya fara da wannan Nassi ɗin ya kuma faɗa masa labari mai daɗi game da Yesu.
Then Philip, opening his mouth, and beginning at this scripture, preached unto him Jesus.
36 Yayinda suke cikin tafiya a kan hanya, sai suka iso wani wurin ruwa bābān nan ya ce, “Duba, ga ruwa. Me zai hana a yi mini baftisma?”
And as they went on their way, they came to a certain water; and the eunuch said: See, here is water: what doth hinder me from being baptized?
And Philip said: If thou believest with all thy heart, thou mayest. And he answering, said: I believe that Jesus Christ is the Son of God.
38 Ya kuwa ba da umarni a tsai da keken yaƙin. Sa’an nan da Filibus da bābān suka gangara zuwa cikin ruwan Filibus kuwa ya yi masa baftisma.
And he commanded the chariot to stand still; and they went down into the water, both Philip and the eunuch: and he baptized him.
39 Sa’ad da suka fita daga cikin ruwan, sai Ruhun Ubangiji ya fyauce Filibus, bābān kuwa bai ƙara ganinsa ba, amma ya ci gaba da tafiyarsa yana farin ciki.
And when they were come up out of the water, the Spirit of the Lord took away Philip; and the eunuch saw him no more. And he went on his way rejoicing.
40 Filibus kuwa ya fito a Azotus, ya yi ta zagawa, yana wa’azin bishara a dukan garuruwan sai da ya kai Kaisariya.
But Philip was found in Azotus; and passing through, he preached the gospel to all the cities, till he came to Caesarea.

< Ayyukan Manzanni 8 >