< Yohanna 1 >
1 Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
2 Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
The same was in the beginning with God.
3 Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
All things were made by him: and without him was made nothing that was made.
4 A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
In him was life, and the life was the light of men.
5 Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
And the light shineth in darkness, and the darkness did not comprehend it.
6 Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
There was a man sent from God, whose name was John.
7 Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
This man came for a witness, to give testimony of the light, that all men might believe through him.
8 Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
He was not the light, but was to give testimony of the light.
9 Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
That was the true light, which enlighteneth every man that cometh into this world.
10 Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
He was in the world, and the world was made by him, and the world knew him not.
11 Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
He came unto his own, and his own received him not.
12 Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
But as many as received him, he gave them power to be made the sons of God, to them that believe in his name.
13 ’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
Who are born, not of blood, nor of the will of the flesh, nor of the will of man, but of God.
14 Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
And the Word was made flesh, and dwelt among us, (and we saw his glory, the glory as it were of the only begotten of the Father, ) full of grace and truth.
15 (Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
John beareth witness of him, and crieth out, saying: This was he of whom I spoke: He that shall come after me, is preferred before me: because he was before me.
16 Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
And of his fulness we all have received, and grace for grace.
17 Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
For the law was given by Moses; grace and truth came by Jesus Christ.
18 Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
No man hath seen God at any time: the only begotten Son who is in the bosom of the Father, he hath declared him.
19 To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
And this is the testimony of John, when the Jews sent from Jerusalem priests and Levites to him, to ask him: Who art thou?
20 Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
And he confessed, and did not deny: and he confessed: I am not the Christ.
21 Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
And they asked him: What then? Art thou Elias? And he said: I am not. Art thou the prophet? And he answered: No.
22 A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
They said therefore unto him: Who art thou, that we may give an answer to them that sent us? What sayest thou of thyself?
23 Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
He said: I am the voice of one crying out in the wilderness, make straight the way of the Lord, as said the prophet Isaias.
24 To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
And they that were sent, were of the Pharisees.
25 suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
And they asked him, and said to him: Why then dost thou baptize, if thou be not Christ, nor Elias, nor the prophet?
26 Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
John answered them, saying: I baptize with water; but there hath stood one in the midst of you, whom you know not.
27 Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
The same is he that shall come after me, who is preferred before me: the latchet of whose shoe I am not worthy to loose.
28 Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
These things were done in Bethania, beyond the Jordan, where John was baptizing.
29 Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
The next day, John saw Jesus coming to him, and he saith: Behold the Lamb of God, behold him who taketh away the sin of the world.
30 Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
This is he, of whom I said: After me there cometh a man, who is preferred before me: because he was before me.
31 Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
And I knew him not, but that he may be made manifest in Israel, therefore am I come baptizing with water.
32 Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
And John gave testimony, saying: I saw the Spirit coming down, as a dove from heaven, and he remained upon him.
33 Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
And I knew him not; but he who sent me to baptize with water, said to me: He upon whom thou shalt see the Spirit descending, and remaining upon him, he it is that baptizeth with the Holy Ghost.
34 Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
And I saw, and I gave testimony, that this is the Son of God.
35 Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
The next day again John stood, and two of his disciples.
36 Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
And beholding Jesus walking, he saith: Behold the Lamb of God.
37 Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
And the two disciples heard him speak, and they followed Jesus.
38 Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
And Jesus turning, and seeing them following him, saith to them: What seek you? Who said to him, Rabbi, (which is to say, being interpreted, Master, ) where dwellest thou?
39 Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
He saith to them: Come and see. They came, and saw where he abode, and they stayed with him that day: now it was about the tenth hour.
40 Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
And Andrew, the brother of Simon Peter, was one of the two who had heard of John, and followed him.
41 Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
He findeth first his brother Simon, and saith to him: We have found the Messias, which is, being interpreted, the Christ.
42 Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
And he brought him to Jesus. And Jesus looking upon him, said: Thou art Simon the son of Jona: thou shalt be called Cephas, which is interpreted Peter.
43 Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
On the following day, he would go forth into Galilee, and he findeth Philip. And Jesus saith to him: Follow me.
44 Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
Now Philip was of Bethsaida, the city of Andrew and Peter.
45 Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
Philip findeth Nathanael, and saith to him: We have found him of whom Moses in the law, and the prophets did write, Jesus the son of Joseph of Nazareth.
46 Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
And Nathanael said to him: Can any thing of good come from Nazareth? Philip saith to him: Come and see.
47 Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
Jesus saw Nathanael coming to him: and he saith of him: Behold an Israelite indeed, in whom there is no guile.
48 Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
Nathanael saith to him: Whence knowest thou me? Jesus answered, and said to him: Before that Philip called thee, when thou wast under the fig tree, I saw thee.
49 Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
Nathanael answered him, and said: Rabbi, thou art the Son of God, thou art the King of Israel.
50 Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
Jesus answered, and said to him: Because I said unto thee, I saw thee under the fig tree, thou believest: greater things than these shalt thou see.
51 Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”
And he saith to him: Amen, amen I say to you, you shall see the heaven opened, and the angels of God ascending and descending upon the Son of man.