< Ayyukan Manzanni 17 >

1 Da suka bi ta Amfifolis da Afolloniya, sai suka isa Tessalonika, inda akwai majami’ar Yahudawa.
Bhakapitilanjeje ku Ampipoli na ku Apolonia, gubhapitengenenje mpaka ku Teshalonike, kweneko jashinkupagwa shinagogi ja Bhayaudi.
2 Kamar yadda ya saba, Bulus ya shiga majami’ar, ranakun Asabbaci uku ya yi ta yin muhawwara da su daga cikin Nassosi,
A Pauli malinga nkubho gwabho gubhailundile, gubhakungulwishe nabhonji ga Majandiko ga Ukonjelo kwa Mobha ga Pumulila gatatu gwangali pumulila.
3 yana musu bayani da tabbatarwa cewa dole Kiristi ya sha wahala ya kuma tashi daga matattu. Ya kuma ce, “Wannan Yesu da nake sanar muku shi ne Kiristi.”
Bhalilunguya na talashiya kuti yashinkupinjikwa a Yeshu bhapotekwe na bhayushe kukopoka kubhawilenje. Na kuti, “A Yeshu bhungunnungushiyangabho ni a Kilishitu.”
4 Waɗansu Yahudawa suka amince suka kuma bi Bulus da Sila, haka ma Hellenawa da yawa masu tsoron Allah da kuma manyan mata ba kaɗan ba.
Bhananji munkumbi gwabhonji gubhakulupalilenje nigubhailundilenje na a Pauli na a Shila. Na Bhagiliki bhabhagwinji bhaajogopangaga a Nnungu na bhanabhakongwe bhakulungwanji, gubhailundilenje.
5 Amma Yahudawa suka yi kishi; saboda haka suka tattara’yan iska daga kasuwa, suka shirya wata ƙungiya, suka tā da tarzoma a birni. Suka ruga zuwa gidan Yason suna neman Bulus da Sila don su kawo su a gaban taron.
Ikabheje Bhayaudi gubhakwetenje lupimililo, gubhapolekenje bhandunji bhangalinginji bha mmbone, gubhatendilenje ulendo nigubhakumbuyenje nnjasha pa shilambo powe. Gubhapitengenenje ku nyumba ja a Yashoni bhaliganishiyanga kuti kweneko shibhaapatanje a Pauli na a Shila nkupinga bhaapelekanje ku lugwinjili lwa bhandu.
6 Amma da ba su same su ba, sai suka ja Yason da waɗansu’yan’uwa zuwa gaban mahukuntan birnin, suna ihu suna cewa, “Waɗannan mutanen da suke tā da fitina ko’ina a duniya sun iso nan,
Ikabheje bhangaapatanga, kwa nneyo gubhaakwekwetenje a Yashoni na bhakilishitu bhananji mpaka ku bhakulungwanji bha shilambo, bhalijobhelanga bhalinkutinji, “Bhene bhandunjibha bhanapuganyanga shilambolyo na nnaino bhaikengenenje na kukuno.
7 Yason kuwa ya karɓe su a gidansa. Dukansu suna karya dokokin Kaisar, suna cewa akwai wani sarki, wanda ake kira Yesu.”
A Yashoni bhashikwaposhelanga kunngwabho. Bhowe bhanakananga Malajilo ga a Kaishali, bhakutinji. ‘Bhapali bhakulungwa bhana bhashemwa a Yeshu.’”
8 Da suka ji haka, sai hankalin taron da na mahukuntan birnin ya tashi.
Kwa gene malobhego, bhakulungwanji bha shilambo na lugwinjili lwa bhandunji gubhatengukenje.
9 Sai suka sa Yason da sauran su biya kuɗin saki sa’an nan suka sallame su.
Gubhaatendilenje a Yashoni na ashaajabhonji bhowe bhashoyanje mmbiya, kungai gubhaaleshilenje bhajabhulangane.
10 Da dare ya yi, sai’yan’uwa suka sallami Bulus da Sila su tafi Bereya. Da suka isa can, sai suka shiga majami’ar Yahudawa.
Ikaishileje shilo, bhakilishitu bhala gubhaapelekenje a Pauli na a Shila mpaka ku Bheloya. Bhakaikanganeje kweneko gubhajinjilenje nshinagogi ja Bhayaudi.
11 Bereyawa kuwa sun fi Tessalonikawa hankali, gama sun karɓi saƙon da marmari ƙwarai, suka kuma yi ta yin bincike Nassosi kowace rana su ga ko abin da Bulus ya faɗa gaskiya ne.
Bhene bhandunjibho pubhalinginji bhanguja kupunda bha ku Teshalonike bhala. Gubhaliposhelenje lilobhe lila kwa ntima gwa mmbone, gubhakaguyenje Majandiko ga Ukonjelo kila lyubha, nkupinga bhalolanje ibhaga ibheleketwa na a Pauli na a Shila ili ya kweli.
12 Yahudawa da yawa suka gaskata, haka ma waɗansu manyan matan Hellenawa da kuma mazan Hellenawa da yawa.
Bhabhagwinji munkumbi gwabhonji mula bhakukulupalilangaga na bhanabhakongwe Bhagiliki bhakwetenje itengu na bhanabhalume bhabhagwinji.
13 Da Yahudawan da suke a Tessalonika suka ji cewa Bulus yana wa’azin maganar Allah a Bereya, sai suka je can ma, suna zuga taro suna kuma tā da hankalinsu.
Ikabheje Bhayaudi bha ku Teshalonike bhakapilikananjeje kuti a Pauli bhanalungaya lilobhe lya a Nnungu ku Bheloya, gubhapitengenenje kweneko, gubhatandubhenje kutenda nnjasha na kukwiya lugwinjili lwa bhandu.
14 Nan da nan’yan’uwa suka sa Bulus yă tafi bakin teku, amma Sila da Timoti suka dakata a Bereya.
Shangu bhakilishitu bhala gubhaapelesheyenje a Pauli mpaka kunyenje litanda, ikabheje a Shila na a Timoteo gubhalepekenje ku Bheloya.
15 Mutanen da suka raka Bulus kuwa suka kawo shi Atens sa’an nan suka dawo da umarnai wa Sila da Timoti cewa su zo wurinsa da gaggawa.
Ikabheje bhaapelesheyenje a Pauli bhala, gubhaapelekenje mpaka ku Atene. Kungai, gubhabhujilenje na ntenga kukopoka kwa a Pauli gwa kuti, a Shila na a Timoteo bhanakabhanje kwaakagula ku Atene.
16 Yayinda Bulus yake jiransu a Atens, ya damu ƙwarai da ya ga birnin cike da gumaka.
A Pauli bhali nkwaalindililanga a Shila na a Timoteo ku Ateneko, yashinkwaashima muntima gwabho bhakaibhoneje yanamu ya ashinnungu igumbele shene shilambo shila.
17 Saboda haka ya yi ta muhawwara a majami’a da Yahudawa da kuma Hellenawa masu tsoron Allah, haka kuma da waɗanda yake tararwa a bakin kasuwa.
Bhai, nshinagogi a Pauli bhatendaga kunguluka na Bhayaudi na bhandunji bhana bhaajogopangaga a Nnungu na kila lyubha bhatendaga tenda nkungulu gwa palugwinjili na bhandunji bhobhowe bhaibhoneyangaga penepo.
18 Wata ƙungiyar Afikuriya da kuma masu bin ussan ilimin Sitoyik suka fara gardama da shi. Waɗansunsu suka ce, “Mene ne mai surutun nan yake ƙoƙarin faɗi?” Waɗansu suka ce, “Kamar yana wa’azin baƙin alloli ne.” Sun faɗa haka ne domin Bulus yana wa’azin labari mai daɗi game da Yesu da kuma tashin matattu.
Na bhananji bhakagulangaga majiganyo ga a Epikulo na a Ashitoiki gubhataukenje. Bhananji bhalinkutinji, “Bhapinga bheleketa nndi bhangumbabha?” Bhananji gubhashiteanje, “Paabhoneka mbuti bhanalunguya ga ashi nnungu bha shijeni.” Pabha a Pauli bhatendaga lunguya ga a Yeshu na ga yuka.
19 Sai suka ɗauke shi suka kawo shi wurin taron Areyofagus, inda suka ce masa, “Ko za mu san mene ne sabon koyarwan nan ya ƙunsa da kake yi?
Kwa nneyo gubhaatolilenje a Pauli gubhaapelekenje ku lukumbi lwa ashikalongolele bha shilambo lwashemwaga Aleopago, gubhashitenje, “Tunapinga tugamanye malombolelo ga majiganyo genu ga shijeni gunkulunguyaga.
20 Kana kawo mana ra’ayoyin da suke baƙo a gare mu, kuma muna so mu san mene ne suke nufi.”
Indu ina itupilikene mmakutu getu inabhoneka ya shijeni kungwetu. Tunapinga tumumanye yene indui malombolelo gakwe nndi.”
21 (Duk Atenawa da baƙin da suke zama a can suna zaman kashe wando ne kawai kuma ba abin da suke yi sai dai taɗi da kuma jin sababbin ra’ayoyi.)
Pabha bhandunji bha ku Atene na bhandunji bhananji bhatamanganaga kweneko bhatendaga pinganga kutagulilana na pilikanishiya ngani ja indu ya shijeni.
22 Sai Bulus ya miƙe tsaye a tsakiyar taron Areyofagus ya ce, “Ya ku mutanen Atens! Na dai lura cewa ta kowace hanya ku masu addini ne ƙwarai.
Bhai, a Pauli gubhajimi pa lukumbi lwa Aleopago, gubhashite, “Mmashilambo bha pa Atene! Pungubhona kuti mmanganyanji nnatolelelanga kwa kaje ngani ja dini,
23 Gama sa’ad da nake zagawa, na lura da kyau da abubuwan da kuke bauta wa, har ma na tarar da wani bagade da wannan rubutu, Ga Allahn da ba a sani ba. To, abin nan da kuke yi wa sujada a matsayin abin da ba ku sani nan ba shi ne zan sanar da ku.
pabha punapitaga ako na koko nikwibhona indu yenunji munkujujilanga Nnungu, njikushibhona shitala shimo shijandishwe. ‘Kwa a Nunngu bhutukakwamanya.’ Bhai, nne ngunakunnungushiyanga, ga bhene a Nnungu bhunkwaatindibhalilanga gwangali kwaamanyabho.
24 “Allahn da ya halicci duniya da kome da yake cikinta shi ne Ubangijin sama da ƙasa, ba ya kuma zama a haikalin da aka gina da hannuwa.
“A Nnungu, bhapengenye shilambolyo na indu yowe ili nkati jakwe, bhashibha Bhakulungwa bha kunnungu na pa shilambolyo, bhalabho bhakatama mmajumba ga jujila Nnungu gashenjilwe na bhandunji.
25 Ba a kuma yin masa hidima da hannun mutum, sai ka ce mai bukatan wani abu, domin shi kansa ne ke ba wa dukan mutane rai da numfashi da kuma kome.
Na wala shakwa shibhaapinga mundu abhatendele mbuti shipali shibhaaloleya, pabha bhenebho ni bhakwaapanganga bhandu bhowe gumi na kwaapanganga kila shindu.
26 Daga mutum ɗaya, ya halicci kowace al’ummar mutane, don su zauna a duk duniya; shi ne kuma ya ƙaddara lokuta bisa ga tsarinsu da kuma inda za su kasance.
Na kukoposhela kuka mundu jumo a Nnungu gubhapengenye bhandunji bha ilambo yowe nikwaatendanga bhajenelanje pa shilambolyo. Bhali bhajibhishile miongwe na mipika ja mmbali ya ilambo ya tama bhene bhandunjibho.
27 Allah ya yi wannan domin mutane su neme shi mai yiwuwa kuma su lalluba su same shi, ko da yake ba shi da nisa daga kowannenmu.
“Bhashinkutenda nneyo, nkupinga bhandunji bha ilambo yowe bhaaloleyanje nkali kwaapapaya papaya, iishile pakwabhona. Nkali nneyo, a Nnungu bhangataliya pubhali tome na uwe.
28 ‘Gama a cikinsa ne muke rayuwa muke motsi muka kuma kasance.’ Yadda waɗansu mawaƙanku suka ce, ‘Mu zuriyarsa ce.’
Malinga shabhelekete mundu jumo, ‘Pabha mututama nkati jabho, tunajima jima, nikola gumi!’ Na malinga bhaajimba bhenunji bhana shibhashite lugulanga. ‘Uwe twaashibhana bhabho’
29 “Saboda haka da yake mu zuriyar Allah ce, kada mu yi tsammani cewa kamannin Allah yana kama da zinariya ko azurfa ko dutse, siffar da mutum ya ƙago ta wurin dabararsa.
Bhai ibhaga, uwe tuli twaashibhana bhabho a Nnungu, tukaapinjikwa kuganishiya kuti Unnungu ulandana na shaabhu, eu ela eu liganga, indu ibheywa kwa lunda lwa bhandunji.
30 A dā Allah ya kawar da Allah ya kawar da kai ga zamanin jahilci, amma yanzu ya umarci dukan mutane a ko’ina su tuba.
Bhai, bhukala gwa ubhelu gwa bhandunji gula a Nnungu bhashinkutenda mbuti bhakakuubhona. Ikabheje nnaino, a Nnungu bhanalajila bhandunji bhowe bha kila mmbali bhaipetanje.
31 Gama ya sa ranar da zai yi wa duniya shari’a da adalci ta wurin mutumin da ya naɗa. Ya riga ya ba da tabbacin wannan ga dukan mutane ta wurin tā da shi daga matattu.”
Pabha bhabhishile lyubha limo lya ukumula bhandunji bha pa shilambolyo gwangali kummonela mundu, kupitila mundu jumo jubhanng'agwile. A Nnungu bhashikong'ondela genego kwa kunnyuya jwene mundujo kukopoka kubhawilenje!”
32 Sa’ad da suka ji maganar tashin matattu, waɗansunsu suka yi tsaki, amma waɗansu suka ce, “Muna so mu ƙara jin ka a kan wannan batu.”
Bhai, bhakaapilikananjeje a Pauli bhalibheleketa ngani ja yuywa bhawilenje, bhananji gubhatendilenje mbenji, ikabheje bhananji gubhashitenje, “Tunapinga tupilikanishiye kabhili jene nganiji.”
33 Da wannan, Bulus ya bar Majalisar.
A Pauli gubhajabhwile, gubhaaleshilenje pa lukumbi pala.
34 Waɗansu mutane kima suka zama mabiyan Bulus suka kuwa gaskata. A cikinsu kuwa akwai Diyonasiyus ɗan Majalisar Areyofagus, haka kuma wata mace mai suna Damaris, da waɗansu dai haka.
Ikabheje bhandunji bhana gubhaakagwilenje na gubhakulupalilenje. Munkumbimo bhaapali a Dionishi bhaaliji bha munkumbi gwa Aleopago na bhakongwe bhamo lina lyabho a Damali na bhananji.

< Ayyukan Manzanni 17 >