< 2 Tessalonikawa 3 >
1 A ƙarshe,’yan’uwa, ku yi mana addu’a domin saƙon Ubangiji yă yi saurin bazuwa a kuma girmama shi, kamar yadda yake a wurinku.
Concerning other things, brothers, pray for us, so that the Word of God may advance and be glorified, just as it is among you,
2 Ku kuma yi addu’a yadda za a cece mu daga mugayen mutane masu mugunta, gama ba kowa ba ne yake da bangaskiya.
and so that we may be freed from pertinacious and evil men. For not everyone is faithful.
3 Ubangiji mai aminci ne, zai ƙarfafa ku, yă kuma tsare ku daga mugun nan.
But God is faithful. He will strengthen you, and he will guard you from evil.
4 Muna da tabbaci cikin Ubangiji cewa kuna bin umarnai da muka yi muku, za ku kuma ci gaba da yin abubuwan da muka umarta.
And we have confidence about you in the Lord, that you are doing, and will continue to do, just as we have instructed.
5 Bari Ubangiji yă bi da zukatanku ga ƙaunan nan ta Allah da kuma jimirin nan na Kiristi.
And may the Lord direct your hearts, in the charity of God and with the patience of Christ.
6 A cikin sunan Ubangiji Yesu Kiristi, muna muku umarni,’yan’uwa, da ku kiyaye kanku daga kowane ɗan’uwa mai zaman banza da ba ya rayuwa bisa ga koyarwar da kuka karɓa daga wurinmu.
But we strongly caution you, brothers, in the name of our Lord Jesus Christ, to draw yourselves away from every brother who is walking in disorder and not according to the tradition that they received from us.
7 Gama ku kanku kun san yadda ya kamata ku bi gurbinmu. Ba mu yi zaman banza sa’ad da muke tare da ku ba,
For you yourselves know the manner in which you ought to imitate us. For we were not disorderly among you.
8 ba mu kuwa ci abincin kowa ba tare da ba mu biya ba. A maimakon haka, mun yi aiki dare da rana, muna fama muna wahala kuma don kada mu nawaita wa waninku.
Nor did we eat bread from anyone for free, but rather, we worked night and day, in hardship and weariness, so as not to be burdensome to you.
9 Mun yi wannan, ba don ba mu da’yancin karɓar irin taimakon nan ba ne, sai dai domin mu zama gurbin da za ku bi.
It was not as if we had no authority, but this was so that we might present ourselves as an example to you, in order to imitate us.
10 Ko ma a sa’ad da muke tare da ku, mun ba ku wannan umarni cewa, “In mutum ya ƙi yin aiki, kada a ba shi abinci.”
Then, too, while we were with you, we insisted on this to you: that if anyone was not willing to work, neither should he eat.
11 Mun ji cewa waɗansunku suna zaman banza. Ba sa aikin kome; sai shisshigi kurum.
For we have heard that there are some among you who act disruptively, not working at all, but eagerly meddling.
12 Irin waɗannan mutane muna ba da umarni muna kuma gargaɗe su cikin Ubangiji Yesu Kiristi su natsu su kuma nemi abincin da suke ci.
Now we charge those who act in this way, and we beg them in the Lord Jesus Christ, that they work in silence and eat their own bread.
13 Game da ku kuma’yan’uwa, kada ku gaji da yin abin da yake daidai.
And you, brothers, do not grow weak in doing good.
14 In wani bai yi biyayya da umarninmu a wannan wasiƙa ba, sai fa ku lura da shi. Kada ku haɗa kai da shi, don yă ji kunya.
But if anyone does not obey our word by this epistle, take note of him and do not keep company with him, so that he may be ashamed.
15 Duk da haka kada ku mai da shi abokin gāba, sai dai ku gargaɗe shi a matsayin ɗan’uwa.
But do not be willing to consider him as an enemy; instead, correct him as a brother.
16 Yanzu, bari Ubangiji mai salama kansa yă ba ku salama a kowane lokaci da kuma a ta kowace hanya. Ubangiji yă kasance tare da ku duka.
Then may the Lord of peace himself give you an everlasting peace, in every place. May the Lord be with all of you.
17 Ni, Bulus, nake rubuta wannan gaisuwa da hannuna, wannan ce shaida a kowace wasiƙata, haka nake rubutu.
The greeting of Paul with my own hand, which is the seal in every epistle. So do I write.
18 Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ku duka.
May the grace of our Lord Jesus Christ be with you all. Amen.