< 2 Sama’ila 24 >

1 Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
And it repeated [the] anger of Yahweh to burn on Israel and he incited David against them saying go count Israel and Judah.
2 Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
And he said the king to Joab - [the] commander of the army who [was] with him go about please in all [the] tribes of Israel from Dan and to Beer Sheba and enroll the people and I will know [the] number of the people.
3 Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
And he said Joab to the king and may he add Yahweh God your to the people like them - and like them a hundred times and [the] eyes of lord my the king [are] seeing [it] and lord my the king why? does he delight in the thing this.
4 Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
And it prevailed [the] word of the king to Joab and over [the] commanders of the army and he went out Joab and commanders of the army before the king to enroll the people Israel.
5 Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
And they passed over the Jordan and they encamped at Aroer [the] south of the city which [is] in [the] middle of the wadi Gad and to Jazer.
6 Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
And they came Gilead towards and to [the] land of Tahtim Hodshi and they came Dan towards Jaan and around to Sidon.
7 Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
And they came [the] fortress of Tyre and all [the] cities of the Hivite[s] and the Canaanite[s] and they went out to [the] Negev of Judah Beer Sheba.
8 Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
And they went about in all the land and they came from [the] end of nine months and twenty day[s] Jerusalem.
9 Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
And he gave Joab [the] number of [the] muster of the people to the king and it was Israel eight hundred thousand man of strength [who] drew a sword and [the] man of Judah [was] five hundred thousand man.
10 Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
And it struck [the] heart of David him after thus he had counted the people. And he said David to Yahweh I have sinned exceedingly [that] which I have done and now O Yahweh take away please [the] iniquity of servant your for I have acted foolishly exceedingly.
11 Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
And he arose David in the morning. And [the] word of Yahweh it came to Gad the prophet [the] seer of David saying.
12 “Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
Go and you will speak to David thus he says Yahweh three [things] I [am] laying on you choose for yourself one from them so I may do [it] to you.
13 Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
And he went Gad to David and he told to him and he said to him ¿ will it come to you seven years - famine - in land your or? three months fleeing you before opponents your and he [will be] pursuing you and or? to be three days pestilence in land your now know and see what? will I bring back [the] [one who] sent me word.
14 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
And he said David to Gad it is distress to me exceedingly let us fall please in [the] hand of Yahweh for [are] great (compassion his *Q(K)*) and in [the] hand of humankind may not I fall.
15 Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
And he gave Yahweh pestilence in Israel from the morning and until a time of an appointed time and he died of the people from Dan and to Beer Sheba seventy thousand man.
16 Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
And he stretched out hand his the angel - Jerusalem to destroy it and he relented Yahweh concerning the harm and he said to the angel the destroyer among the people enough now let drop hand your and [the] angel of Yahweh he was near [the] threshing floor of (Araunah *Q(K)*) the Jebusite.
17 Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
And he said David to Yahweh when saw he - the angel - who was striking down the people and he said here! I (the shepherd *X*) I have sinned and I I have done wrong and these the sheep what? have they done let it be please hand your on me and on [the] house of father my.
18 A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
And he came Gad to David on the day that and he said to him go up raise up to Yahweh an altar on [the] threshing floor of (Araunah *Q(K)*) the Jebusite.
19 Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
And he went up David according to [the] word of Gad just as he had commanded Yahweh.
20 Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
And he looked down Araunah and he saw the king and servants his passing on to him and he went out Araunah and he bowed down to the king face his [the] ground towards.
21 Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
And he said Araunah why? has he come lord my the king to servant his and he said David to buy from with you the threshing floor to build an altar to Yahweh so it may be restrained the plague from on the people.
22 Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
And he said Araunah to David let him take and let him offer up lord my the king the good (in eyes his *Q(K)*) see the ox[en] for the burnt offering and the threshing-sledges and [the] equipment of the ox[en] for the wood.
23 Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
Everything he gives Araunah O king to the king. And he said Araunah to the king Yahweh God your may he accept favorably you.
24 Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
And he said the king to Araunah In-deed certainly I will buy [it] from you for a price and not I will offer up to Yahweh God my burnt offerings without paying and he bought David the threshing floor and the ox[en] for silver shekels fifty.
25 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.
And he built there David an altar to Yahweh and he offered up burnt offerings and peace offerings and he was entreated Yahweh for the land and it was restrained the plague from on Israel.

< 2 Sama’ila 24 >