< 2 Sama’ila 23 >

1 Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
And these [are] [the] words of David last [the] utterance of David [the] son of Jesse and [the] utterance of the man [who] he was raised up height [the] [one] anointed of [the] God of Jacob and [the] pleasant [one] of [the] songs of Israel.
2 “Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
[the] spirit of Yahweh he has spoken by me and speech his [is] on tongue my.
3 Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
He said [the] God of Israel to me he spoke [the] rock of Israel [one who] rules over humankind righteous [one who] rules [the] fear of God.
4 yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
And like [the] light of morning [when] it dawns [the] sun morning not clouds from brightness from rain vegetation from [the] earth.
5 “Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
For not thus [is] house? my with God for a covenant of perpetuity he has made to me arranged in everything and preserved for all salvation my and every desire for not will he make grow?
6 Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
And a worthless person [is] like thorn[s] [which is] chased away all of them for not in a hand people will take.
7 Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
And anyone [who] he will touch them he will arm himself iron and [the] wood of a spear and with fire certainly they will be burned at the dwelling.
8 Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
These [are] [the] names of the warriors who [belonged] to David Josheb-Basshebeth a Tahkemonite - [the] chief of the three he Adino (the Eznite *Q(K)*) on eight hundred [one] slain at a time (one. *Q(K)*)
9 Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
(And [was] after him *Q(k)*) Eleazar [the] son of (Dodo *Q(K)*) [the] son of Ahoah among three (the warriors *Q(K)*) with David when defied they the Philistines [who] they were gathered there for battle and they went up [the] man of Israel.
10 amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
He he arose and he struck down among the Philistines until - for it was weary hand his and it cleaved hand his to the sword and he did Yahweh a deliverance great on the day that and the people they returned after him only to strip.
11 Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
And [was] after him Shamma [the] son of Agee [the] Hararite and they were gathered [the] Philistines to Lehi and it was there [the] portion of the field full of lentils and the people it fled from before [the] Philistines.
12 Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
And he took his stand in [the] middle of the portion and he delivered it and he struck down [the] Philistines and he did Yahweh a deliverance great.
13 A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
And they went down (three *Q(K)*) from the thirty leader[s] and they came to [the] harvest to David to [the] cave of Adullam and a community of Philistines [was] encamped in [the] valley of [the] Rephaites.
14 Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
And David then [was] in the stronghold and a garrison of Philistines then [was] Beth-lehem.
15 Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
And he desired David and he said who? will he give to drink me water from [the] well of Beth-lehem which [is] at the gate.
16 Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
And they broke through [the] three the warriors in [the] camp of [the] Philistines and they drew water from [the] well of Beth-lehem which [was] at the gate and they carried [it] and they brought [it] to David and not he was willing to drink them and he poured out them to Yahweh.
17 Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
And he said far be it to me O Yahweh than to do I this [thing] ¿ [the] blood of the men who went with lives their and not he was willing to drink them these [things] they did [the] three the warriors.
18 Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
And Abishai [the] brother of - Joab [the] son of Zeruiah he [was] [the] chief (of the three *Q(K)*) and he he wielded spear his on three hundred [one] slain and [belonged] to him a name among the three.
19 Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
More than the three ¿ for [was he] honored and he became to them a commander and to the three not he came.
20 Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
And Benaiah [the] son of Jehoiada [was] a son of a man (of strength *Q(K)*) great of deeds from Kabzeel he he struck down [the] two [the] lion-like men of Moab and he he went down and he struck down (the lion *Q(K)*) in [the] midst of the pit on [the] day of the snow.
21 Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
And he he struck down a man Egyptian (a man of *Q(K)*) appearance and [was] in [the] hand of the Egyptian a spear and he went down to him with the staff and he seized the spear from [the] hand of the Egyptian and he killed him with own spear his.
22 Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
These [things] he did Benaiah [the] son of Jehoiada and [belonged] to him a name among three the warriors.
23 Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
More than the thirty [he was] honored and to the three not he came and he appointed him David to bodyguard his.
24 Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
Asah-el [the] brother of Joab [was] among the thirty Elhanan [the] son of Dodo Beth-lehem.
25 Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
Shammah the Harodite Elika the Harodite.
26 Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
Helez the Paltite Ira [the] son of Ikkesh the Tekoite.
27 Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
Abiezer the Anathothite Mebunnai the Hushathite.
28 Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
Zalmon the Ahohite Maharai the Netophathite.
29 Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
Heleb [the] son of Baanah the Netophathite. Ittai [the] son of Ribai from Gibeah of [the] descendants of Benjamin.
30 Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
Benaiah [the] Pirathonite Hiddai from [the] wadis of Gaash.
31 Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
Abi-Albon the Arbathite Azmaveth the Barhumite.
32 Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
Eliahba the Shaalbonite [the] sons of Jashen Jonathan.
33 ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
([the] son of *X*) Shammah the Hararite Ahiam [the] son of Sharar the Hararite.
34 Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
Eliphelet [the] son of Ahasbai [the] son of the Maacathite. Eliam [the] son of Ahithophel the Gilonite.
35 Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
(Hezrai *Q(K)*) the Carmelite Paarai the Arbite.
36 Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
Igal [the] son of Nathan from Zobah. Bani the Gadite.
37 Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
Zelek the Ammonite. Naharai the Beerothite ([the] bearer of *Q(K)*) [the] armor of Joab [the] son of Zeruiah.
38 Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
Ira the Ithrite Gareb the Ithrite.
39 da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.
Uriah the Hittite all [were] thirty and seven.

< 2 Sama’ila 23 >