< 2 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
David sang HERREN denne Sang, dengang HERREN havde frelst ham af alle hans Fjenders og af Sauls Haand.
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
Han sang: »HERRE, min Klippe, min Borg, min Befrier,
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
min Gud, mit Bjerg, hvortil jeg tyr, mit Skjold, mit Frelseshorn, mit Værn, min Tilflugt, min Frelser, som frelser mig fra Vold!
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
Jeg paakalder HERREN, den Højlovede, og frelses fra mine Fjender.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Dødens Brændinger omsluttede mig, Ødelæggelsens Strømme forfærdede mig,
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
Dødsrigets Reb omspændte mig, Dødens Snarer faldt over mig; (Sheol h7585)
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
i min Vaande paakaldte jeg HERREN og raabte til min Gud. Han hørte min Røst fra sin Helligdom, mit Raab fandt ind til hans Ører!
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
Da rystede Jorden og skjalv, Himlens Grundvolde bæved og rysted, thi hans Vrede blussede op.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Røg for ud af hans Næse, fortærende Ild af hans Mund, Gløder gnistrede fra ham.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
Han sænkede Himlen, steg ned med Skymulm under sine Fødder;
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
baaret af Keruber fløj han, svæved paa Vindens Vinger;
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
han omgav sig med Mulm som en Bolig, mørke Vandmasser, vandfyldte Skyer.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
Fra Glansen foran ham for der Hagl og Ildgløder ud.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
HERREN tordned fra Himlen, den Højeste lod høre sin Røst;
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
han udslynged Pile, adsplittede dem, lod Lynene funkle og skræmmede dem.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
Havets Bund kom til Syne, Jordens Grundvolde blottedes ved HERRENS Trusel, for hans Vredes Pust.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
Han udrakte Haanden fra det høje og greb mig, drog mig op af de vældige Vande,
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
frelste mig fra mine mægtige Fjender, fra mine Avindsmænd; de var mig for stærke.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
Paa min Ulykkes Dag faldt de over mig, men HERREN blev mig et Værn.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
Han førte mig ud i aabent Land, han frelste mig, thi han havde Behag i mig.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
HERREN gengældte mig efter min Retfærd, lønned mig efter mine Hænders Uskyld;
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
thi jeg holdt mig til HERRENS Veje, svigted i Gudløshed ikke min Gud;
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
hans Bud stod mig alle for Øje, jeg veg ikke fra hans Love.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
Ustraffelig var jeg for ham og vogtede mig for Brøde.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
HERREN lønned mig efter min Retfærd, mine Hænders Uskyld, som var ham for Øje!
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
Du viser dig from mod den fromme, retsindig mod den retsindige,
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
du viser dig ren mod den rene og vrang mod den svigefulde.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
De arme giver du Frelse, hovmodiges Øjne Skam!
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
Ja, du er min Lampe, HERRE! HERREN opklarer mit Mørke.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
Thi ved din Hjælp søndrer jeg Mure, ved min Guds Hjælp springer jeg over Volde.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
Fuldkommen er Guds Vej, lutret er HERRENS Ord. Han er et Skjold for alle, der sætter deres Lid til ham.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Ja, hvem er Gud uden HERREN, hvem er en Klippe uden vor Gud,
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
den Gud, der omgjorded mig med Kraft, jævnede Vejen for mig,
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
gjorde mine Fødder som Hindens og gav mig Fodfæste paa Højne,
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
oplærte min Haand til Krig, saa mine Arme spændte Kobberbuen?
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
Du gav mig din Frelses Skjold, din Nedladelse gjorde mig stor;
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
du skaffede Plads for mine Skridt, mine Ankler vaklede ikke.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Jeg jog mine Fjender, indhentede dem, vendte først om, da de var gjort til intet,
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
slog dem ned, saa de ej kunde rejse sig, men laa faldne under min Fod.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Du omgjorded mig med Kraft til Kampen, mine Modstandere tvang du i Knæ for mig;
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
du slog mine Fjender paa Flugt mine Avindsmænd ryddede jeg af Vejen.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
De raabte, men ingen hjalp, til HERREN, han svared dem ikke.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Jeg knuste dem som Jordens Støv, som Gadeskarn tramped jeg paa dem.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Du friede mig af Folkekampe, du satte mig til Folkeslags Høvding; nu tjener mig ukendte Folk;
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Udlandets Sønner kryber for mig; blot de hører om mig, lyder de mig:
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Udlandets Sønner vansmægter, kommer skælvende frem af deres Skjul.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
HERREN lever, højlovet min Klippe, ophøjet være min Frelses Gud,
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
den Gud, som giver mig Hævn, lægger Folkeslag under min Fod
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
og frier mig fra mine Fjender! Du ophøjer mig over mine Modstandere, fra Voldsmænd frelser du mig.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
HERRE, derfor priser jeg dig blandt Folkene og lovsynger dit Navn,
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
du, som kraftig hjælper din Konge og viser din Salvede Miskundhed. David og hans Æt evindelig.«

< 2 Sama’ila 22 >