< 1 Sama’ila 2 >

1 Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
Da bad Hanna og sagde: Mit Hjerte jubler over HERREN, mit Horn er løftet ved min Gud, min Mund vidt opladt mod mine Fjender, jeg glæder mig over din Frelse.
2 “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
Der er ingen Hellig som HERREN, nej, der er ingen uden dig, der er ingen Klippe som vor Gud!
3 “Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
Vær varsomme med eders store Ord, Frækhed undslippe ej eders Mund! Thi en vidende Gud er HERREN, og Gerninger vejes af ham.
4 “An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
Heltes Bue er brudt, men segnende omgjorder sig med Kraft;
5 Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
mætte lader sig leje for Brød, men sultnes Slid hører op; den ufrugtbare føder syv, men den med de mange vansmægter.
6 “Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol h7585)
HERREN døder, gør levende, fører ned i Dødsriget og fører op; (Sheol h7585)
7 Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
HERREN gør fattig, gør rig, han nedbøjer, og han ophøjer;
8 Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
han rejser ringe af Støvet, af Skarnet løfter han fattige for at bænke og give dem Ærespladsen. Thi HERRENS er Jordens Søjler, Jorderig bygged han paa dem!
9 Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
Han vogter sine frommes Skridt, men gudløse omkommer i Mørket; thi ingen vinder Sejr ved egen kraft.
10 waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
HERREN — hans Fjender forfærdes, den Højeste tordner i Himmelen, HERREN dømmer den vide Jord! Han skænker sin Konge Kraft, løfter sin Salvedes Horn!
11 Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
Saa drog hun til Rama, men Drengen gjorde Tjeneste for HERREN under Præsten Elis Tilsyn.
12 ’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
Men Elis Sønner var Niddinger; de ænsede hverken HERREN
13 Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
eller Præstens Ret over for Folket. Hver Gang en Mand bragte et Slagtoffer, kom Præstens Tjener, medens Kødet kogte, med en tregrenet Gaffel i Haanden
14 zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
og stak den ned i Karret, Krukken, Kedelen eller Gryden, og alt, hvad Gaffelen fik med op, tog Præsten for sin Del. Saaledes bar de sig ad over for alle de Israeliter, som kom til Silo for at ofre der.
15 Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
Eller ogsaa kom Præstens Tjener, før de bragte Fedtet som Røgoffer, og sagde til Manden, som ofrede: »Giv Præsten Kød til at stege; han tager ikke mod kogt Kød af dig, kun raat!«
16 In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
Sagde Manden nu til ham: »Først maa Fedtet bringes som Røgoffer, bagefter kan du tage saa meget, du lyster!« svarede han: »Nej, giv mig det nu, ellers tager jeg det med Magt!«
17 Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
Og de unge Mænds Synd var saare stor for HERRENS Aasyn, idet de viste Ringeagt for HERRENS Offergaver.
18 Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
Imidlertid gjorde Samuel Tjeneste for HERRENS Aasyn; og Drengen var iført en linned Efod.
19 Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
Hans Moder lavede hvert Aar en lille Kappe til ham og bragte ham den, naar hun drog op med sin Mand for at ofre det aarlige Offer.
20 Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
Og Eli velsignede Elkana og hans Hustru og sagde: »HERREN give dig Afkom af denne Kvinde til Gengæld for ham, hun overlod HERREN!« Saa gik de hjem igen.
21 Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
Og HERREN saa til Hanna, og hun blev frugtsommelig og fødte tre Sønner og to Døtre. Men Drengen Samuel voksede op hos HERREN.
22 To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
Eli var meget gammel, og da han hørte, hvorledes hans Sønner behandlede hele Israel, og at de laa hos Kvinderne, som gjorde Tjeneste ved Indgangen til Aabenbaringsteltet,
23 Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
sagde han til dem: »Hvorfor gør I saadanne Ting, som jeg hører alt Folket tale om?
24 A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
Bær eder dog ikke saaledes ad, mine Sønner! Thi det er ikke noget godt Rygte, jeg hører gaa fra Mund til Mund i HERRENS Folk.
25 In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
Naar en Mand synder mod en anden, dømmer Gud dem imellem; men synder en Mand mod HERREN, hvem kan da optræde som Dommer til Gunst for ham?« Men de brød sig ikke om deres Faders Advarsel, thi HERREN vilde deres Død.
26 Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
Men Drengen Samuel voksede til og gik stadig frem i Yndest baade hos HERREN og Mennesker.
27 Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
Da kom en Guds Mand til Eli og sagde: Saa siger HERREN: »Se, jeg aabenbarede mig for dit Fædrenehus, dengang de var Trælle for Faraos Hus i Ægypten,
28 Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
og jeg udvalgte det af alle Israels Stammer til at gøre Præstetjeneste for mig, til at træde op paa mit Alter for at tænde Offerild og til at bære Efod for mit Aasyn; og jeg tildelte dit Fædrenehus alle Israeliternes Ildofre.
29 Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
Hvor kan du da se ondt til mit Slagtoffer og Afgrødeoffer, som jeg har paabudt, og ære dine Sønner fremfor mig, idet I gør eder til gode med det bedste at alle mit Folk Israels Offergaver!
30 “Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
Derfor lyder det fra HERREN, Israels Gud: Vel har jeg sagt, at dit Hus og dit Fædrenehus for stedse skulde færdes for mit Aasyn; men nu, lyder det fra HERREN, være det langt fra mig! Nej, dem, som ærer mig, vil jeg ære, og de, som ringeagter mig, skal beskæmmes.
31 Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
Se, den Tid skal komme, da jeg, afhugger din og dit Fædrenehus's Arm, saa ingen i dit Hus skal blive gammel;
32 Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
og du skal se ondt til alt det gode, HERREN gør mod Israel, og ingen Sinde skal nogen i din Slægt blive gammel.
33 Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
Kun en eneste af din Slægt vil jeg undlade at bortrydde fra mit Alter for at lade hans Øjne hentæres og hans Sjæl vansmægte: men alle de andre i din Slægt skal dø for Menneskers Sværd.
34 “‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
Og det Tegn, du faar derpaa, skal være det, der overgaar dine to Sønner Hofni og Pinehas: Paa een Dag skal de begge dø.
35 Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
Men jeg vil udvælge mig en trofast Præst; han skal handle efter mit Hjerte og mit Sind, og ham vil jeg bygge et varigt Hus, saa han altid skal færdes for min Salvedes Aasyn.
36 Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”
Da skal enhver, som er tilbage af din Slægt, komme og kaste sig til Jorden for ham for at faa en Skilling eller en Skive Brød, og han skal sige: Und mig dog Plads ved et af dine Præsteskaber, for at jeg kan have en Bid Brød at spise!«

< 1 Sama’ila 2 >