< 2 Bitrus 2 >

1 Amma a dā akwai annabawan ƙarya a cikin mutane, kamar yadda za a sami malaman ƙarya a cikinku. A ɓoye za su shigar da karkataccen koyarwa mai hallaka, har ma su yi mūsun Ubangiji mai iko duka wanda ya saye su suna kawo wa kansu hallaka farat ɗaya.
Men falske Propheter voro ock ibland folket, som ock ibland eder varda skola falske lärare; hvilke med ibland införa skola förderfvelig partier, och förneka Herran, som dem köpt hafver; och skola föra öfver sig sjelfva en hastig fördömelse.
2 Da yawa za su bi hanyoyinsu na rashin kunya su kuma sa a rena hanyar gaskiya.
Och månge skola efterfölja deras förderf; genom hvilka sanningenes väg blifver försmädd;
3 Cikin kwaɗayinsu waɗannan malaman ƙarya za su cuce ku da tatsuniyoyin da suka ƙaga. Hukuncinsu yana a rataye a kansu tun da daɗewa, hallakarsu kuma ba ta barci.
Och uti girighet, med diktad ord, skola de handla med eder; hvilkom domen nu längesedan icke sen är, och deras fördömelse sofver icke.
4 Gama in har Allah bai ƙyale mala’iku sa’ad da suka yi zunubi ba, amma ya tura su cikin lahira, domin a tsare su don hukunci; (Tartaroō g5020)
Ty hafver Gud icke skonat Änglomen, som syndade, utan hafver dem med mörksens kedjor nederkastat till helvetes, öfverantvardandes till att förvaras till domen; (Tartaroō g5020)
5 in har bai ƙyale duniya ta dā ba sa’ad da ya kawo ambaliya a kan mutanenta marasa tsoron Allah, amma ya kiyaye Nuhu, mai wa’azin adalci, da kuma waɗansu bakwai;
Och hafver icke skonat den förra verldene; utan bevarat Noe, rättfärdighetenes Predikare, sjelf åttonde, och lät floden gå öfver de ogudaktigas verld;
6 in har ya hukunta biranen Sodom da Gomorra ta wurin ƙone su suka zama toka, ya kuma maishe su misali na abin da zai faru da marasa tsoron Allah;
Och hafver gjort de städer Sodoma och Gomorra till asko, omstört och fördömt dem; och satt för ett efterdömelse dem ogudaktigom, som sedan komma skulle;
7 in kuwa har ya ceci Lot, mai adalci, wanda ya damu ainun da ƙazamar rayuwar mutane marasa bin doka;
Och hafver frälst den rättfärdiga Lot, som var plågad af skamliga menniskor, genom deras sköraktiga umgängelse;
8 (adon kuwa abin da adalin nan ya yi, ya kuma gani, sa’ad da yake a cikinsu, sai kowace rana yakan ji ciwon aikinsu na kangara a zuciyarsa mai adalci)
Ty efter han var rättfärdig, och bodde ibland dem, och måste dock sådana se och höra, plågade de dageligen den rättfärdiga själen med sina onda gerningar.
9 in haka ne, to, Ubangiji ya san yadda zai ceci mutane masu tsoron Allah daga gwaje-gwaje, yă kuma tsare marasa adalci don ranar hukunci, har yă zuwa ranar shari’a.
Herren kan frälsa de gudaktiga utaf frestelsen, men behålla de orättfärdiga till domedag, till att pinas;
10 Wannan gaskiya ce musamman ga waɗanda suke bin sha’awace-sha’awacen lalaci na mutuntaka, suna kuma rena masu mulki. Da ƙarfin hali da kuma girman kai, waɗannan mutane ba sa tsoro kawo zargin ɓata sunan talikan sama;
Men aldramest dem som vandra efter köttet, uti orenom lusta, och försmå herrskapet, öfverdådige, ensinnade, och intet rädas försmäda väldigheterna;
11 duk da haka ko mala’iku ma da suka fi su ƙarfi suka kuma fi su iko, ba sa kawo irin wannan zargi na ɓata suna game da waɗannan talikai a gaban Ubangiji.
Ändock Änglarna, som i kraftene och starkhetene större äro, icke draga kunna den försmädeliga domen emot sig, af Herranom.
12 Amma waɗannan mutane suna yin saɓo a kan abubuwan da ba su fahimta ba. Suna kama da dabbobi marasa hankali, halittun da suke bin abin da jikinsu ya faɗa musu kawai, waɗanda aka haifa don a kama a hallaka, kuma kamar dabbobi su ma za su hallaka.
Men de äro såsom de oförnuftiga djur, som af naturen dertill födda äro, att de skola fångna och slagtade varda; försmäda det de intet förstå, och skola uti sitt förderfveliga väsende förgås;
13 Za a yi musu sakamako da muguntar da suka yi. A ra’ayinsu jin daɗi shi ne a yi annashuwa da rana tsaka. Su ƙazamai ne marasa kunya, suna cike da jin daɗin sha’awace-sha’awacensu yayinda suke cin biki tare da ku.
Och få orättfärdighetenes lön. De hållat för vällust, att de lefva i timeliga kräselighet; de äro slemheter och skamfläckar; pråla af edra gåfvor, slösa med edart;
14 Idanunsu sun cike da zina, ba sa ƙoshi da yin zunubi; suna jarrabtar waɗanda ba tsayayyu ba; gwanaye ne a kan kwaɗayi, la’anannun iri!
Hafva ögonen full med horeri, låta icke förmena sig syndena, och locka till sig de ostadiga själar; hafva sin hjerta genomöfvad i girighet; förbannadt folk;
15 Sun bar miƙaƙƙiyar hanya suka bauɗe suna bin hanyar Bala’am ɗan Beyor, wanda ya yi ƙaunar hakkin mugunta.
Öfvergifva rätta vägen, och gå ville, och efterfölja Balaams, Bosors sons väg, hvilken älskade vrånghetenes lön.
16 Amma an tsawata masa saboda laifinsa ta wurin jaki, dabbar da ba ta magana, wadda ta yi magana da muryar mutum ta kuma kwaɓi haukan annabin.
Men han blef straffad för sin vrånghet; det stumma arbetsdjuret talade med menniskoröst, och förtog Prophetens galenskap.
17 Waɗannan mutane maɓulɓulai ne babu ruwa da kuma hazon da guguwar iska take kora. An shirya matsanancin duhu dominsu.
De äro källor utan vatten, och molnskyr, som af vädret drifvas; hvilkom förvaradt är ett svart mörker, till evig tid. (questioned)
18 Gama suna surutai banza na girman kai, ta wurin son bin fasikanci na mutuntaka, sukan jan hankulan mutanen da suke kuɓucewa daga waɗancan masu zama cikin kuskure.
Ty de tala stolt ord, som äro fåfäng: och igenom otukt locka dem till köttslig lusta, som rättsliga undsluppne voro, och ännu vandra i villfarelse;
19 Suna yin musu alkawarin’yanci, yayinda su kansu bayi ne ga aikin lalata gama mutum bawa ne ga duk abin da ya mallake shi.
Och lofva dem frihet, ändock de sjelfve äro förderfvelsens tjenare; ty af hvem någor öfvervunnen varder, hans tjenare är han vorden.
20 In har sun kuɓuta daga lalacin duniya ta wurin sanin Ubangijinmu da kuma Mai Cetonmu Yesu Kiristi sai suka sāke koma a cikin lalacin, har ya rinjaye su, za su fi muni a ƙarshe fiye da farko.
Ty sedan de, genom Herrans och Frälsarens Jesu Christi kunskap, undflytt hafva verldenes orenlighet, och hafva åter bevefvat sig deruti, och äro öfvervunne, är dem det yttersta värre vordet än det första.
21 Zai fi musu kyau da ba su taɓa sanin hanyar adalci ba, fiye da a ce sun sani sa’an nan su juya bayansu ga umarni mai tsarkin nan da aka ba su.
Och hade dem bättre varit intet förståndit rättfärdighetenes väg, än, sedan de förstodo, vända sig ifrå det helga budet, som de anammat hade.
22 A kansu karin maganan nan gaskiya ce, “Kare ya koma kan amansa,” da kuma, “Alade da aka yi wa wanka, ya koma birgimarsa cikin laka.”
Dem är vederfaret det som för ett sant ordspråk plägar sägas: Hunden går åter till sina spyo; och svinet, som tvaget är, sölar sig åter i träcken.

< 2 Bitrus 2 >